• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Na Dauke Da Nauyin Dakatar Da Kisan Fararen Hula A Rafah

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da dubban Falasdinawa dake arewacin zirin Gaza ke tserewa zuwa kudanci, sakamakon yakin da sojojin Isra’ila suka kaddamar na murkushe kungiyar Hamas tun daga ranar 7 ga watan Oktoban bara, masharhanta da dama na ganin lokaci na kara kurewa, na kawo karshen wannan tashin hankali, duba da cewa ga alama matakan sojin da Isra’ilan ke dauka ba abu ne da zai kare a nan kusa ba.

Ya zuwa yanzu, hare-haren sojojin Isra’ila sun kora sama da mutune miliyan guda wani lungu dake kudancin Gaza, inda birnin Rafah ya zamo “Gaba kura baya sayaki” ga masu tserewa hare-haren Isra’ila.

  • Xi Jinping Ya Nanata Wajibcin Yin Kwaskwarima Da Kirkire-Kirkire Cikin Hakikanin Hali A Lardin Hunan
  • Majasirdin Sarkin Zazzau, Alhaji Yusuf Saleh Barde Ya Rasu

Duk da jan hankali da aka sha yi masa, firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya dage cewa sai sojojinsa sun kaddamar da hare-hare a Rafah. Alkaluma sun nuna cewa, kafin wannan tashin hankali, Rafah na da kimanin mutane 275,000 ne kacal, amma yanzu mutane sama da miliyan 1.4 ke cunkushe a cikinsa, a yanayi na matukar bukatar jin kai.

Majalissar Dinkin Duniya, da kungiyar tarayyar Turai ta EU, sun nuna damuwa game da mummunan tasirin da hare-hare a Rafah za su yi ga fararen hula. A daya hannun kuma, a baya bayan nan ita ma kasar Sin ta bayyana damuwa, game da yadda rikicin Falasdinu da Isra’ila ya haura watanni 5, kana yanayin jin kai a wurin ke kara tabarbarewa, don haka ta bayyana wajibcin gaggauta tsagaita wuta nan take, da yin iyakacin kokarin kiyaye rayukan fararen hula, da kuma rage matsalolin jin kai.

Mun san dai da fari, Amurka na sahun gaba wajen marawa Isra’ila baya a wannan yaki mai muni, amma a yanzu ta fara sauya matsaya, har ma an jiyo shugaba Joe Biden na Amurkan na cewa, kaiwa birnin Rafah hare-hare zai zama kuskure mai matukar muni.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

La’akari da goyon baya da Amurkan ta nunawa Isra’ila tsawon lokaci kan wannan batu, ta hanyar maimaita dakatar da kudurin kwamitin tsaron MDD game da tsagaita wuta a Gaza, da tarin makamai da ta rika aikewa Isra’ila, da ma yadda kalaman sauya matsayar ta suka fara sanya Isra’ilan nuna alamun sassautawa. Muna iya cewa idan akwai wani karfi da zai iya sauya yanayin da ake ciki a Gaza ba zai wuce Amurka ba. Ko da yake wasu masu sharhi sun ce gwamnatin Amurka mai ci ta fara sauya matsaya ne saboda al’ummunta sun fara bore, inda a baya bayan nan masu zanga-zanga a jihar Michigan, suka rika daga kyallaye masu dauke da sakon “Idan ba a dakatar da wuta ba, ba za a yi zabe ba”.

Koma dai mene ne ke faruwa a siyasar cikin gidan Amurka? Abun da ya fi damun al’ummun duniya masu son zaman lafiya, shi ne fatan ganin Amurka ta yi abun da ya dace, ta saurari ra’ayoyin sauran sassa, ta kuma goyi bayan dakatar da bude wuta a Gaza, da wanzar da zaman lafiya mai dorewa a yankin gabas ta tsakiya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Direba Da Fasinjoji 18 A Katsina

Next Post

CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 2

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

2 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

4 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

4 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

8 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

10 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

10 hours ago
Next Post
CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1

CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 2

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.