• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaron Iyakoki: ACG James Sunday Ya Jagoranci Taron Samar Da Dabarun Aiki A Jos

by Sadiq
2 years ago
Iyakoki

A wani yunkuri na inganta tsaron iyakokin Nijeriya da magance kalubalen tsaro a Arewa Maso Gabas, Kodinetan shiyyar C na Hukumar Shige Da Fice ta Kasa (NIS), ACG James Sunday, ya jagoranci wani muhimmin taro a Jos, babban birnin Jihar Filato.  

Taron ya samu halartar Kwanturololin jihohin Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Yobe, da kuma Jihar Filato.

  • Zulum Ya Rabawa ‘Yan Sa Kai Da Mafarauta 5,523 Naira Miliyan 255 Da Buhunan Shinkafa 5,513
  • Majasirdin Sarkin Zazzau, Alhaji Yusuf Saleh Barde Ya Rasu

Shiyya C, kasancewarta daya daga cikin shiyyoyi takwas masu muhimmanci ga hukumar NIS, na taka muhimmiyar rawa a harkokin tsaron kasa, musamman idan aka yi la’akari da matsalolin tsaro da suka addabi yankin Arewa maso Gabas.

Iyakoki

ACG James Sunday ya jaddada bukatar karfafa kokarin da ake na ganin an samar da tsaro a iyakokin kasar nan, musamman bisa ga umarnin da Shugaba Tinubu ya bayar na sake bude iyakokin Nijeriya da Nijar.

LABARAI MASU NASABA

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Bayan taron, an cimma yarjejeniya tsakanin Kwanturololin, na daukar sabbin dabaru da matakan tsaro a kan iyakoki, tare da jaddada hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro.

Iyakoki

Kazalika, Kodinetan ya nuna muhimmancin hadin kai a tsakanin mataimakin gwamnan Jihar Filato, jami’an gwamnati da hukumomin soji a Jos.

ACG James Sunday ya sake nanata kudurin tabbatar da tsarin ‘Ba sani ba sabo’ a fannin kula da iyaka, kamar yadda mai girma ministan harkokin cikin gida ya bayar da umarni.

Abu mafi jan hankali a taron shi ne taron kam tsaron iyakokin Arewa Maso Gabas da Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum zai jagoranta.

Iyakoki

Taron wanda aka shirya gudanarwa a Maiduguri, na da nufin hada kan masu ruwa da tsaki, ciki har da masu sarautar gargajiya, domin magance matsalar tsaro gaba daya a yankin.

Iyakoki

Domin tabbatar da tsaro da ayyukan hadin gwiwa na kasa, ACG James Sunday da tawagarsa sun jaddada muhimmancin goyon bayan masu ruwa da tsaki a matakai daban-daban don tabbatar da tsaro ga kasa baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m
Labarai

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

November 10, 2025
Next Post
Afirka

Kwararrun Afirka Sun Nuna Yabo Ga Dimokuradiyyar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

November 10, 2025
FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

November 10, 2025
Xi Ya Taya Ouattara Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Cote D’Ivoire

Xi Ya Taya Ouattara Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Cote D’Ivoire

November 10, 2025
Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

November 10, 2025
Xi Ya Halarci Bikin Bude Gasar Wasanni Ta Sin Karo Na 15 A Guangzhou

Xi Ya Halarci Bikin Bude Gasar Wasanni Ta Sin Karo Na 15 A Guangzhou

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.