• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Wuya Bankuna 17 Cikin 24 Su Mallaki Sabon Jari Da CBN Ya Tsara -Rahoto

by Bello Hamza
2 years ago
CBN

Wani sabon rahoto daga kamfanin ‘’Ernst and Young’’ ya kiyasata cewa, bankuna 17 ne kawai daga cikin bankuna 24 da ake da su a Nijeriya za su iya tsallake sabon ka’idar da Babban Bankin Nijeriya ya kirikiro na cewa dole kowanne banki ya mallaki jarin akalla Naira biliyan 25 kafin ya ci gaba da gudanar da hakokinsa na bankin a Nijeriya. Wannan yana nuni da cewa, an yi karin ninki 15 na matakin jarin da ake da shi baya.

Rahoton ya kuma tattauna hanyoyi da mafita ga bankunan da suka kasa cika ka’idar jari da CBN ya gidaya.

  • An Fara Taron Kasa Da Kasa Kan Tsarin Dimokuradiyya Karo Na Uku A Nan Birnin Beijing
  • Ɗiawara Ya Fice Daga Tawagar Faransa Bayan An Hana ‘Yan Wasa Yin Azumi

Rahoton ya kuma tabbatar da cewa, bangaren banki na Nijeriya suna nan daram ba tare da wata barazanar da za ta iya haifar da wata fargaba ba. An fara aiwatar da irin wannan tsarin kayyade jari ne a shekarar 2023.

Rahoton ya kuma bayyana cewa, wannan sabon tsarin jari da CBN ya ayyana zai kai ga hadewar wasu bankunan abin da ake kira da ‘Mergers and Ackuisitions (M&A)’, kamar yadda aka gani a lokacin da aka daga jarin bankuna a shekarar 2004 zuwa 2005. A wancan lokacin bankunan sun tashi daga 89 zuwa 25.

Rahoton ya kuma ce, “Duk da cewa, Gwamnan Babban Bankin bai yi nuni da yadda karin jarin zai shafi yadda bankuna suke gudanar da harkokinsu ba, amma an yi amfani ne da fannoni uku na tattalin arziki  da kuma yadda tattalin arzikin Nijeriya ke tafiya a halin yanzu. Ta haka ne muka iya gano bankunan da ba za su iya tsallake wannan siradin ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

“A yadda abubuwa ke tafiya a halin yanzu musamman ganin an nunka jarin da ake nema daga bankuna har sau 15 to lallai bankuna 17 daga cikin bankuna 24 da muke da su ba za su iya samar da mafi karancin jari da CBN ya bullo da shi ba.”

Rahoton ya kuma yi nuni da cewa, shirin kara jarin bankuna ya taso ne bayan da aka karya darajar naira a wannan shekarar, ya kuma ce, a shekarar 2005 da aka yi irin wannan daga jarin bankunan, darajar naira na a matsayin N132.9 a kan Dalar Amurka 1 amma a wannan lokacin ana samu Dala 1 na Amurka ne a kan fiye da N1400.

A watan Nuwamba na shekarar 2023 ne Gwamnan Babban Bankin Nijeriya nuna sha’war kara yawan jarin da bankuna za su mallaka, ya ce, yin haka zai taimaka wajen tsaftace bangaren bankuna tare da daga darajar naira wanda hakan zai taimaka wa tattalin arzikin kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Next Post
Yadda Ta Kaya A Wasan Sada Zumunci Tsakanin Nijeriya Da Ghana

Yadda Ta Kaya A Wasan Sada Zumunci Tsakanin Nijeriya Da Ghana

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.