ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Wuya Bankuna 17 Cikin 24 Su Mallaki Sabon Jari Da CBN Ya Tsara -Rahoto

by Bello Hamza
2 years ago
CBN

Wani sabon rahoto daga kamfanin ‘’Ernst and Young’’ ya kiyasata cewa, bankuna 17 ne kawai daga cikin bankuna 24 da ake da su a Nijeriya za su iya tsallake sabon ka’idar da Babban Bankin Nijeriya ya kirikiro na cewa dole kowanne banki ya mallaki jarin akalla Naira biliyan 25 kafin ya ci gaba da gudanar da hakokinsa na bankin a Nijeriya. Wannan yana nuni da cewa, an yi karin ninki 15 na matakin jarin da ake da shi baya.

Rahoton ya kuma tattauna hanyoyi da mafita ga bankunan da suka kasa cika ka’idar jari da CBN ya gidaya.

  • An Fara Taron Kasa Da Kasa Kan Tsarin Dimokuradiyya Karo Na Uku A Nan Birnin Beijing
  • Ɗiawara Ya Fice Daga Tawagar Faransa Bayan An Hana ‘Yan Wasa Yin Azumi

Rahoton ya kuma tabbatar da cewa, bangaren banki na Nijeriya suna nan daram ba tare da wata barazanar da za ta iya haifar da wata fargaba ba. An fara aiwatar da irin wannan tsarin kayyade jari ne a shekarar 2023.

ADVERTISEMENT

Rahoton ya kuma bayyana cewa, wannan sabon tsarin jari da CBN ya ayyana zai kai ga hadewar wasu bankunan abin da ake kira da ‘Mergers and Ackuisitions (M&A)’, kamar yadda aka gani a lokacin da aka daga jarin bankuna a shekarar 2004 zuwa 2005. A wancan lokacin bankunan sun tashi daga 89 zuwa 25.

Rahoton ya kuma ce, “Duk da cewa, Gwamnan Babban Bankin bai yi nuni da yadda karin jarin zai shafi yadda bankuna suke gudanar da harkokinsu ba, amma an yi amfani ne da fannoni uku na tattalin arziki  da kuma yadda tattalin arzikin Nijeriya ke tafiya a halin yanzu. Ta haka ne muka iya gano bankunan da ba za su iya tsallake wannan siradin ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

“A yadda abubuwa ke tafiya a halin yanzu musamman ganin an nunka jarin da ake nema daga bankuna har sau 15 to lallai bankuna 17 daga cikin bankuna 24 da muke da su ba za su iya samar da mafi karancin jari da CBN ya bullo da shi ba.”

Rahoton ya kuma yi nuni da cewa, shirin kara jarin bankuna ya taso ne bayan da aka karya darajar naira a wannan shekarar, ya kuma ce, a shekarar 2005 da aka yi irin wannan daga jarin bankunan, darajar naira na a matsayin N132.9 a kan Dalar Amurka 1 amma a wannan lokacin ana samu Dala 1 na Amurka ne a kan fiye da N1400.

A watan Nuwamba na shekarar 2023 ne Gwamnan Babban Bankin Nijeriya nuna sha’war kara yawan jarin da bankuna za su mallaka, ya ce, yin haka zai taimaka wajen tsaftace bangaren bankuna tare da daga darajar naira wanda hakan zai taimaka wa tattalin arzikin kasa.

CBN
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
Yadda Ta Kaya A Wasan Sada Zumunci Tsakanin Nijeriya Da Ghana

Yadda Ta Kaya A Wasan Sada Zumunci Tsakanin Nijeriya Da Ghana

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.