• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barnar Da Isra’ila Ke Ci Gaba Da Yi A Gaza

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tashin hankali da cin zarafin da Yahudawa ke yi a kan yankin Gaza da ke Gabas ta tsakiya ya fara tada zuciyar duk wani dan adam ba tare da bambancin yankin da ya fito ba ko addininsa ko kuma irin akidar siyasar da yake yi. Duk da irin munin abin da muke gani na tashin hankali a kasar Yukrain kadan wannan kadan ne a kan abin da yake faruwa na rashin imani a kan al’ummar Falasdinawa na yankin Gaza, na nuna karfin da Isra’ila ke yi a kan al’ummar Falasdin da sunan yaki da kungiyar Hamas.

Wannan yakin na baya-bayan nan ya fara ne a ranar 7 ga watan Oktoba 2023, bayan da kungiyar Hamas ta kai wani wawan hari a cikin kasar Isra’ila inda suka samu nasarar kashe wasu mutane da dama suka kuma yi garkuwa da wasu . Wannan harin ya matukar kunyata Isra’ila wadda take da tunanin ba zai yiwu a kai masu irin wanna harin ba saboda karfin jami’an tsaronta da kuma yadda ta yi suna a duniya na cewa ita kasa ce mai karfin sojoji da kuma rundunar leken asiri mafi inganci a duniya amma dakarun Hamas suka shiga har cikin Isra’ila suka yi masu ta’asar da ta kunyata su sosai a idon duniya.

  • Sharhi: Shin Isra’Ila Za Ta Yi Biyayya Ga Hukuncin Kotun Duniya Game Da Yakin Gaza?
  • Turmutsitsin Rabon Tallafi Da Zakka: Yadda Mutum 10 Suka Rasu A Bauchi Da Nasarawa

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, halin da Gaza ke ciki a wannna lokacin ba lokaci ne na neman wanda yake da laifi ba, duk da cewa, wasu na ganin ai kungiyar Hamas ce ta fara kai hari a kan Is’ra’ila a wannan karon, a harin da suka kai a ranar 7 ga watan Oktoba na shekarar 2023, amma kuma wannan cin zalin ya yi yawa. A kan haka ne ma Sakataren tsaron Amurka,Lloyd James Austin, ya bayyana cewa, ko Isra’ila ta shafe Hamas daga doron kasa ne ba wata gwaninta ta yi ba, ita ce dai ta yi asara.

Abin da ke faruwa a Gaza a halin yanzu abu ne da ya zama kalubale ga duk wani da ke da halin bayar da gudunmawar ganin an dakatar da yakin ya kuma kasa, saboda haka ya kamata dukkan wani mai yi wa duniya fatan alhairi ya kawo tasa gudummawar don ganin an dakatar da cin zalin da Yahudawa ke yi wa al’ummar Faladinawa na kashe kananan yara da mata a kullun garin Allah ya waye.

Duk da cewa, ana iya yin Allah wadai da abin da dakarun Hamas suka yi na kai hari a ranar 7 ga watan Oktoba 2023 amma kuma martanin da Yahudawa ke mayarwa a kan zirin Gaza zuwa yanzu babu hankali a cikin shi, abu ne da Shugaban Kasar Amurka Joe Biden, ya nuna a matsayin rashin hankali ya kuma nuna rashin jin dadinsa a kan yadda Isra’ila ke ta kashe al’umma babu kakkautawa.

Labarai Masu Nasaba

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Ba za mu bari siyasar da ke tattare da lamarin rikicin Falasdinawa ta dauke mana hankali ba.Gaza, wani yanki ne da ke da al’umma Falasdinawa masu tarin yawa suna kuma ganin dole Yahudawa ‘yan kama wuri zauna su bar masu yankinsu, amma kuma abin lura a nan shi ne, Yahudawa da Faladinawa dukkan su daga tsatso daya ne na Annabi Ibrahim a kan haka ne ya kamata su fahimci cewa, dole su yi hakuri da juna su zauna da juna lafiya a matsayin kasa biyu masu ‘yanci, kowa ya mutunta abokan zamansa.

A wannan halin ana iya cewa, fada ne a tsakanin ‘yan uwa, amma kuma a halin yanzu fadan yana neman daukar wani sabon salo da ya zama dole duniya ta tsayu don ganin an kawo karshen rasa rayukan da ake yi.

A ra’ayinmu, abin da yake faruwa a Gaza yana fito da munafuncin kasashen Larabawa ne, daga dukkan alamu kasashen Larabawa basu son ganin an kawo karshen wannan yakin. Sun gwammace su rika hankoron kai agajin abinci da sauran su, wannan lamarin bayar da gudummawa ganin an kawo karshen yakin Babban dalilin su na kin tsayuwar ganin an kawo karshen yakin, wani abu ne da kowa ya sani.

Haka kuma rikicin na Gaza ya kara bayyana munafuncin kasar Amurka wadda ta yi watsi da ra’ayoyin kasashen duniya ta ci gaba da ba Yahudawa goyon baya a yakin da take yi da al’ummar Falasdinawa.

Ba kowa ne yake maraba da matsayar Amurka a wannan rikicin ba musamman ganin yadda take dakile duk wani kokarin da kasashen duniya suke yi na ganin an kawo karshen cin zalin da Yahudawa suke yi wa mata da kananan yara a zirin Gaza,kowa ya san yadda Amurka ke ba Yahudawa makaman yaki da kuma yadda take kawar da kai ga laifukkan yaki da Yahudawa ke aikatawa a zirin Gaza.

A ra’ayinmu yakin da ake yi a Gaza da kuma wanda ake yi a Yukrain sun kara bayyana cikakken munafincin kasar Amurka, hakanan kuma munafincin Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana, a halin yanzu sun zama ‘yan amshin shata, basu da wani tasiri a idon duniya domin da kansu suke dakile duk wani kokarin da ake yi na kawo karshen cin zarafin al’umma.

Duk da wannan halin da ake ciki muna kira ga al’ummar duniya maza da mata daga dukkan bangarori ba tare da bambancin siyasa ko na addini ba, su hada hannu su tabbatar da an kawo karshen cin zarafin bil adam a Gaza. Tabbas wannan yakin ba zai amfani kowa daga bangarorin Falasdinawa da Yahudawa ba gaba daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Allah (SWT) Ya Alakanta Kansa Da Azumi

Next Post

Tsananin Zafin Rana Na Janyo Mana Cutar Daji – Shugaban Zabaya Na Kaduna

Related

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

57 minutes ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

2 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

5 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

6 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

7 hours ago
Next Post
Zabaya

Tsananin Zafin Rana Na Janyo Mana Cutar Daji - Shugaban Zabaya Na Kaduna

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.