ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Shin Isra’Ila Za Ta Yi Biyayya Ga Hukuncin Kotun Duniya Game Da Yakin Gaza?

by CGTN Hausa
2 years ago
Isra'ila

A ranar Juma’a ne kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICJ) wanda aka fi sani da kotun duniya ta ba Isra’ila umarni guda shida dangane da kisan kiyashi da take yi a Gaza, amma babu batun tsagaita bude wuta a cikin umarnin a bayyane.

 

An sanar da matakin na gaggawa ne a daidai lokacin da kotun ta yi zama kan shari’ar kisan kiyashin da kasar Afirka ta Kudu ta shigar a kan Isra’ila, wanda ta saurari shaidu a farkon wannan watan. Afirka ta Kudu ta bayyana abin da Isra’ila ke aikatawa a Gaza a matsayin kisan kare dangi amma Isra’ila ta musanta zargin, tana mai cewa yakinta a Gaza ya samo asali ne daga yunkurin “kare kai”, kuma ya zama dole ta kawar da Hamas. Ta kuma jaddada cewa ba za ta kawo karshen yakin ba har sai ta cimma wannan buri.

ADVERTISEMENT
  • Micheal Keating: Kasar Sin Ba Barazanar Tattalin Arziki Ba Ce
  • Masana’antun Kauyukan Sin Sun Samu Ci Gaba Yadda Ya Kamata A Shekarar 2023

Kusan watanni hudu ke nan duniya tana kallon yadda ake ruguza Gaza, lamarin da ya haifar da rikicin jin kai da ba a taba ganin irinsa ba. Ba a taba ganin irin wannan zaluncin da gangan ba a duniya, tare da nuna kyama ga kimar dan Adam da rayuwar dan Adam, yayin da wasu daga cikin manyan kasashen duniya suka ci gaba da siyasantar da batun.

 

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Kotun duniya ta yi umarni ga Isra’la kamar haka, dole ne Isra’ila ta dauki duk matakan da za a iya dauka don hana aikata abubuwa kamar yadda aka zayyana a cikin mataki na 2 na yarjejeniyar hana kisan kare dangi ta 1948. Wanda ya kunshi hana kashe mambobin wata kungiya, hana haifar da cutarwa ta jiki ko ta hankali ga mambobin wannan kungiyar, hana haifar da yanayin rayuwa wadanda za su kai ga kawo karshen wanzuwar wata al’umma, da kuma hana aiwatar da ayyukan da aka tsara don hana haifuwa a cikin wannan rukunin mutane. Dole ne Isra’ila ta tabbatar da cewa sojojinta ba su aiwatar da ko daya daga cikin wadannan matakan ba ga Falasdinawa ba.

 

Umarnin ya ci gaba da cewa, dole ne Isra’ila ta hana tare da hukunta wani tunani ko jama’a da suka shirya yin kisan kare dangi dangane da mambobin kungiyar Falasdinu a zirin Gaza”. Dole ne Isra’ila ta tabbatar da isar da muhimman ayyuka da kuma muhimman kayan agajin jin kai ga fararen hula a Gaza. Dole ne Isra’ila ta hana lalata shaidun laifukan yaki a Gaza tare da ba da damar gudanar da bincike na gaskiya. Dole ne Isra’ila ta gabatar da rahoto kan duk matakan da ta dauka don yin biyayya ga matakan da kotun ta dauka a cikin wata daya da yanke hukuncin.

To tambayar ita ce, shin Isra’ila za ta yi biyayya ga kotun duniya dangane da wannan hukunci? Tuni dai Isra’ila ta halaka Falasdinawa sama da 26,000 a hare-haren da take kaiwa kan zirin Gaza. Tare da katse hanyoyin sadarwa, da ta samar da abinci da agajin jin kai, da magunguna da ruwan sha. (Muhammed Yahaya)

Isra'ila
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Afirka Da Sin Suna Da Matsaya Daya Wato Kare Zaman Lafiya Da Adalci

Afirka Da Sin Suna Da Matsaya Daya Wato Kare Zaman Lafiya Da Adalci

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.