ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Shin Isra’Ila Za Ta Yi Biyayya Ga Hukuncin Kotun Duniya Game Da Yakin Gaza?

by CGTN Hausa
2 years ago
Isra'ila

A ranar Juma’a ne kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICJ) wanda aka fi sani da kotun duniya ta ba Isra’ila umarni guda shida dangane da kisan kiyashi da take yi a Gaza, amma babu batun tsagaita bude wuta a cikin umarnin a bayyane.

 

An sanar da matakin na gaggawa ne a daidai lokacin da kotun ta yi zama kan shari’ar kisan kiyashin da kasar Afirka ta Kudu ta shigar a kan Isra’ila, wanda ta saurari shaidu a farkon wannan watan. Afirka ta Kudu ta bayyana abin da Isra’ila ke aikatawa a Gaza a matsayin kisan kare dangi amma Isra’ila ta musanta zargin, tana mai cewa yakinta a Gaza ya samo asali ne daga yunkurin “kare kai”, kuma ya zama dole ta kawar da Hamas. Ta kuma jaddada cewa ba za ta kawo karshen yakin ba har sai ta cimma wannan buri.

ADVERTISEMENT
  • Micheal Keating: Kasar Sin Ba Barazanar Tattalin Arziki Ba Ce
  • Masana’antun Kauyukan Sin Sun Samu Ci Gaba Yadda Ya Kamata A Shekarar 2023

Kusan watanni hudu ke nan duniya tana kallon yadda ake ruguza Gaza, lamarin da ya haifar da rikicin jin kai da ba a taba ganin irinsa ba. Ba a taba ganin irin wannan zaluncin da gangan ba a duniya, tare da nuna kyama ga kimar dan Adam da rayuwar dan Adam, yayin da wasu daga cikin manyan kasashen duniya suka ci gaba da siyasantar da batun.

 

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Kotun duniya ta yi umarni ga Isra’la kamar haka, dole ne Isra’ila ta dauki duk matakan da za a iya dauka don hana aikata abubuwa kamar yadda aka zayyana a cikin mataki na 2 na yarjejeniyar hana kisan kare dangi ta 1948. Wanda ya kunshi hana kashe mambobin wata kungiya, hana haifar da cutarwa ta jiki ko ta hankali ga mambobin wannan kungiyar, hana haifar da yanayin rayuwa wadanda za su kai ga kawo karshen wanzuwar wata al’umma, da kuma hana aiwatar da ayyukan da aka tsara don hana haifuwa a cikin wannan rukunin mutane. Dole ne Isra’ila ta tabbatar da cewa sojojinta ba su aiwatar da ko daya daga cikin wadannan matakan ba ga Falasdinawa ba.

 

Umarnin ya ci gaba da cewa, dole ne Isra’ila ta hana tare da hukunta wani tunani ko jama’a da suka shirya yin kisan kare dangi dangane da mambobin kungiyar Falasdinu a zirin Gaza”. Dole ne Isra’ila ta tabbatar da isar da muhimman ayyuka da kuma muhimman kayan agajin jin kai ga fararen hula a Gaza. Dole ne Isra’ila ta hana lalata shaidun laifukan yaki a Gaza tare da ba da damar gudanar da bincike na gaskiya. Dole ne Isra’ila ta gabatar da rahoto kan duk matakan da ta dauka don yin biyayya ga matakan da kotun ta dauka a cikin wata daya da yanke hukuncin.

To tambayar ita ce, shin Isra’ila za ta yi biyayya ga kotun duniya dangane da wannan hukunci? Tuni dai Isra’ila ta halaka Falasdinawa sama da 26,000 a hare-haren da take kaiwa kan zirin Gaza. Tare da katse hanyoyin sadarwa, da ta samar da abinci da agajin jin kai, da magunguna da ruwan sha. (Muhammed Yahaya)

Isra'ila
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Afirka Da Sin Suna Da Matsaya Daya Wato Kare Zaman Lafiya Da Adalci

Afirka Da Sin Suna Da Matsaya Daya Wato Kare Zaman Lafiya Da Adalci

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.