• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sabbin Gwamnoni 13 Suka Lafto Wa Jihohinsu Bashin Biliyan 226 Cikin Wata 6

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnoni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla sabbin gwamnonin jihohin Nijeriya 13 ne suka karbi bashi biliyan 226.8 a cikin gida da waje cikin watanni shida kacal bayan sun hau karagar mulkin jihohinsu daban-daban, kamar yadda rahoton hukumar kula da basuka (DM0) ta fitar.

Rahoton hukumar DMO ya yi amfani da kididdigar basukan waje bisa la’akari da canjin dala kai naira 889.

  • Bayar Da Tallafin Wutar Lantarki Kaso 85 na Kara Nuna Tinubu Mai Kishin Jama’a Ne – Minista
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Gargadi Manoman Kan Sayar Da Kayan Aikin Da Ta Ba Su

Basukan wadanda suka hada da rancen cikin gida da masu ba da lamuni na kasa da kasa irinsu babban bankin duniya da kuma asusun bayar da lamuni ta duniya (IMF).

Rahoton hukumar DMO ta wallafa a shafinta zuwa ranar 20 ga watan Disamba 20 da 30 June 2023 ne aka kiyasce wannan adadin basukan.

Jerin jihohin da suka lafto wannan makudan kudaden a matsayin rance su ne, Jihar Benuwai, Kurus Ribas, Katsina, Neja, Filato, Ribas, Zamfara da kuma babban birnin tarayya wadanda suka samu biliyan 115.57 daga hannun masu ba da lamunin na cikin gida, yayin da gwamnonin Ebonyi, Kaduna, Kano, Neja, Filato, Sakwato, Taraba da Zamfara suka ciwo basukan dala miliyan 125.1, kimanin naira biliyan 111.24 daga masu ba da rance na waje.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

Rahoton ya ci gaba da ba da bayani da cewa gwamnan Kurus Ribas, Bassey Out shi ne ya ciwo bashi mafi yawa a tsakanin wannan lokacin da ya kai naira biliyan 16.2, na bashin cikin gida da kuma dala miliyan 57.95 daga masu ba da lamuni na waje a tsakanin watan June zuwa Disamban 2023. Gwamnan Jihar Katsina ne ya biyo bayansa da ciwo bashin naira biliyan 36.93 da ya karu daga biliyan 62.37 zuwa biliyan 99.2 a watan Disamban 2023.

Jiha ta uku kuwa ita ce Jihar Neja da ta ciwo bashin cikin gida na naira biliyan 17.85 da ya karu daga biliyan 121.95 a June na 2023 zuwa biliyan 139.8 a watan Disamba.

Jihar Filato kuwa, bashin naira biliyan 16.32 ta ciwo, Ribas ta lafto wa kanta rancen naira biliyan 7.07, Zamfara kuwa naira biliyan 14.26 ta ciyo, yayin da birnin tarayya a karkashin jagorancin Nyesom Wike ta ciwo bashin naira biliyan 6.75 daga masu ba da lamuni na cikin gida.

A basukan waje kuwa, gwamna Jihar Ebnonyi, Francis Nwifuru ya amshi bashin dala miliyan 37.54, yayin da gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani ya karbi dala miliyan 17.69 daga masu ba da lamuni na waje.

Bugu da kari, gwamnonin Kano ya ci bashin dala miliyan 6.6, Neja dala miliyan 1.27, Filato dala 831,008, Sakkwato dala 499,472, Taraba dala miliyan 1.51, da kuma Zamfara mai bashin dala 655,563 daga masu ba da rance na waje.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Tafi Legas Don Gudanar Da Bikin Sallah

Next Post

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3 A Kaduna

Related

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
Labarai

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

29 minutes ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

1 hour ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

4 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

14 hours ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

15 hours ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

17 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Hallaka 'Yan Bindiga 3 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

July 30, 2025
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.