ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sabbin Gwamnoni 13 Suka Lafto Wa Jihohinsu Bashin Biliyan 226 Cikin Wata 6

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gwamnoni

Akalla sabbin gwamnonin jihohin Nijeriya 13 ne suka karbi bashi biliyan 226.8 a cikin gida da waje cikin watanni shida kacal bayan sun hau karagar mulkin jihohinsu daban-daban, kamar yadda rahoton hukumar kula da basuka (DM0) ta fitar.

Rahoton hukumar DMO ya yi amfani da kididdigar basukan waje bisa la’akari da canjin dala kai naira 889.

  • Bayar Da Tallafin Wutar Lantarki Kaso 85 na Kara Nuna Tinubu Mai Kishin Jama’a Ne – Minista
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Gargadi Manoman Kan Sayar Da Kayan Aikin Da Ta Ba Su

Basukan wadanda suka hada da rancen cikin gida da masu ba da lamuni na kasa da kasa irinsu babban bankin duniya da kuma asusun bayar da lamuni ta duniya (IMF).

ADVERTISEMENT

Rahoton hukumar DMO ta wallafa a shafinta zuwa ranar 20 ga watan Disamba 20 da 30 June 2023 ne aka kiyasce wannan adadin basukan.

Jerin jihohin da suka lafto wannan makudan kudaden a matsayin rance su ne, Jihar Benuwai, Kurus Ribas, Katsina, Neja, Filato, Ribas, Zamfara da kuma babban birnin tarayya wadanda suka samu biliyan 115.57 daga hannun masu ba da lamunin na cikin gida, yayin da gwamnonin Ebonyi, Kaduna, Kano, Neja, Filato, Sakwato, Taraba da Zamfara suka ciwo basukan dala miliyan 125.1, kimanin naira biliyan 111.24 daga masu ba da rance na waje.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Rahoton ya ci gaba da ba da bayani da cewa gwamnan Kurus Ribas, Bassey Out shi ne ya ciwo bashi mafi yawa a tsakanin wannan lokacin da ya kai naira biliyan 16.2, na bashin cikin gida da kuma dala miliyan 57.95 daga masu ba da lamuni na waje a tsakanin watan June zuwa Disamban 2023. Gwamnan Jihar Katsina ne ya biyo bayansa da ciwo bashin naira biliyan 36.93 da ya karu daga biliyan 62.37 zuwa biliyan 99.2 a watan Disamban 2023.

Jiha ta uku kuwa ita ce Jihar Neja da ta ciwo bashin cikin gida na naira biliyan 17.85 da ya karu daga biliyan 121.95 a June na 2023 zuwa biliyan 139.8 a watan Disamba.

Jihar Filato kuwa, bashin naira biliyan 16.32 ta ciwo, Ribas ta lafto wa kanta rancen naira biliyan 7.07, Zamfara kuwa naira biliyan 14.26 ta ciyo, yayin da birnin tarayya a karkashin jagorancin Nyesom Wike ta ciwo bashin naira biliyan 6.75 daga masu ba da lamuni na cikin gida.

A basukan waje kuwa, gwamna Jihar Ebnonyi, Francis Nwifuru ya amshi bashin dala miliyan 37.54, yayin da gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani ya karbi dala miliyan 17.69 daga masu ba da lamuni na waje.

Bugu da kari, gwamnonin Kano ya ci bashin dala miliyan 6.6, Neja dala miliyan 1.27, Filato dala 831,008, Sakkwato dala 499,472, Taraba dala miliyan 1.51, da kuma Zamfara mai bashin dala 655,563 daga masu ba da rance na waje.

Gwamnoni
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Hallaka 'Yan Bindiga 3 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.