ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Kwara Ta Gargadi Manoman Kan Sayar Da Kayan Aikin Da Ta Ba Su

by Abubakar Abba
2 years ago
kwara

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Gwamnatin Jihar Kwara, ta kaddamar da rabon kayan aikin gona ga manoma ‘yan asalin jihar su kimanin 2,019, inda ta gargade su a kan sayar da kayan da ta raba musu, domin amfanin kawunansu.

An gudanar da rabon wadannan kayan gona ne a garin Ilorin, wanda kuma yana daya daga cikin zango na uku na daukin aikin Fadama ‘CARES’ na gwamnatin jihar.

  • CISLAC Ta Gudanar Da Taro A Kano Kan Canjin Yanayi A Nijeriya
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Mutane 12 Da Dukiyar Miliyan 130 A Kano

Wasu daga cikin kayan da aka raba wa manoman sun hada da, injinan ban ruwa da abincin kajin gidan gona da sauran makamantansu.

ADVERTISEMENT

A yayin kaddamar da rabon kayan, Gwamnan Jihar AbdulRahman AbdulRazak ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta sama wa manoma wannan dauki ne, domin rage musu radadin tattalin arzikin da suke fuskanta tare kuma da yakar yunwa da talauci a daukacin fadin jihar baki-daya.
AbdulRahman ya ci gaba da bayyana cewa, gwamnatin jihar za ta tabbatar da ci gba da bibiyar kayan, domin manoman da suka amfana su su yi amfani da su yadda ya dace ba tare da sun sayarwa mutane daban ba.
Gwamnan, wanda shugaban kwamitin shiri na Fadama a jihar, Mista Ishiak Olayinka Oloruko-Oba ya wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa, ana sa ran aikin da manoman da suka amfana shi, zai taimakawa daukacin al’ummar jihar baki-daya.
A nasa jawabin tun da farko, jami’in shirin na ‘Fadama CARES’ na Jihar Kwara Fadama, Dakta Busari Toyin Isiaka ya bayyana cewa, shirin na daya daga cikin daukin annobar Korona da kuma kokarin sake farfado da tattalin arziki.
A cewar AbdulRahman, “A yau muna raba wa manoma su kimanin 2,019 wannan tallafi, inda ya kara da cewa, a shekarar 2022, manoma guda 6,561 ne suka amfana da shi, inda kuma manoma guda 8,020, suka fito a kashi na biyu.”
Daya daga cikin wadnda suka amfana da wadannan kayayyaki, akwai Kwamarade Jamiu Ahmed inda ya bayyana cewa, dukkanin daukacin wadannan kaya sun zo ne a kan gaba, inda kuma ya yi alkawarin yin amfani da kayan yadda ya dace.

kwara
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Aiwatar Da Kudurin MDD Na Tsagaita Bude Wuta A Gaza

Kasar Sin Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Aiwatar Da Kudurin MDD Na Tsagaita Bude Wuta A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.