• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Amurka Na Dakile Cinikayyar Ababen Hawa Masu Aiki Da Lantarki Na Sin Za Su Haifar Da Koma Bayan Cinikayya A Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Matakan Amurka Na Dakile Cinikayyar Ababen Hawa Masu Aiki Da Lantarki Na Sin Za Su Haifar Da Koma Bayan Cinikayya A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

A baya bayan nan, gwamnatin Amurka ta sanar da shirin ta na gudanar da bincike kan ababen hawa masu amfani da lantarki kirar kasar Sin da ake shigarwa kasar, bisa fakewa da batun tsaron kasa, yayin da a daya hannun ita ma kungiyar tarayyar Turai EU, ta fitar da wasu ka’idoji dake umartar bangaren jami’an kwastam, da ya rika yin rajistar irin wadannan ababen hawa kirar kasar Sin da ake shigarwa nahiyar.

Game da hakan, sassa masu ruwa da tsaki daga ma’aikatar raya masana’antu da fasahar sadarwar Sin, sun yi tsokaci da cewa, akwai wasu kasashe da yankuna, wadanda ba tare da wata kwakkwarar hujja ba, suna aiwatar da ka’idojin sanya shingen cinikayya ga ababen hawa masu amfani da lantarki kirar kasar Sin, wanda hakan ya sabawa dokokin cinikayyar kasa da kasa na kungiyar cinikayya ta duniya WTO, kuma hakan zai yi matukar illata ayyukan masana’antu masu nasaba, da ma tsarin shigar da ababen hawa sassan duniya daban daban, tare da cutar da moriyar masu sayayyar hajojin. Bangaren na Sin ya tabbatar da cewa, wannan mataki zai kuma haifar da tafiyar hawainiya ga matakan wasu kasashe, na sauya akala zuwa amfani da makamashin lantarki a ababen hawa.

Jami’an ma’aikatar, sun kara da cewa, a shekarun baya bayan nan, Sin na nacewa hanyar samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da rage fitar da iskar carbon mai dumama yanayi, da samar da ci gaba mai dorewa. Kana kasar na aiwatar da matakan yayata ci gaban fasahohi, da gina masana’antu masu bin tsarin kare muhallin halittu, da samarwa sassan kasa da kasa hajoji masu araha, nau’o’i daban daban, da ababen hawa masu amfani da sabbin makamashi, da kayayyakin sarrafawa, da sassan kayan gyara, da sauran abubuwan bukata a fannin. Hakan ya gabatarwa duniya da kwarewa ta zahiri, ya kuma samar da sabon mafari mai karfi a fannin raya amfani da sabbin makamashi a ababen hawa a duniya baki daya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Amsa Tambayoyi Game Da Ziyarar Da Sakatariyar Baitil-malin Amurka Ta Gudanar A Sin

Next Post

Dalilin Haramta Tafiyar Dare A Iyakokinmu Da Katsina Da Sokoto – Gwamnatin Zamfara

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

27 minutes ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

31 minutes ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

2 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

4 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

4 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

6 hours ago
Next Post
Dalilin Haramta Tafiyar Dare A Iyakokinmu Da Katsina Da Sokoto – Gwamnatin Zamfara

Dalilin Haramta Tafiyar Dare A Iyakokinmu Da Katsina Da Sokoto – Gwamnatin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.