• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Sallar Idi A Gombe

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Yadda Aka Gudanar Da Sallar Idi A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya tare da Sarkin Gombe, Alhaji (Dakta) Abubakar Shehu Abubakar III, gami da dubban al’ummar musulmai ne suka gudanar da Sallar Idi mai raka’a biyu a jihar da ke alamta kammala Azumin watan Ramadana.

Mataimakin babban limamin Gombe, Ustaz Aliyu Hammari, shi ne ya jagoranci Sallar wacce ta hada fuskokin dubban jama’a da jami’an gwamnati, kakakin majalisar jihar da sauransu.

  • Sakon Sallah: Gwamna Nasir Ya Yi Kira Da Hadin Kai Don Gina Jihar Kebbi
  • Gidauniyar Saraki Ta Kammala Shirin Rabon Abincin Buda-baki

Kazalika, bayan kammala Sallar Idin an gudanar da hawan sallah cikin kasaita da kyale-kyale domin nuna murna da farin ciki da wannan Idin.

A sakonsa na sallah ga al’ummar musulmai, Gwamnan Jihar Gombe, kuma Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya al’ummar Musulmin jihar murnar bikin Sallar Idi, yayin da suka bi sahun takwarorinsu na faɗin duniya don alamta ƙarshen azumin watan Ramadan mai alfarma.

A sakonsa na fatan alheri dauke da sanya hannun kakakinsa Malam Ismaila Uba Misilli, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci Musulmai su kiyaye koyarwa da dabi’un da suka koya a cikin watan na Ramadan, tare da ɗabbaƙasu a cikin rayuwarsu ta yau da kullum don ci gaban al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

Gombe

Ya jawo hankalin al’ummar jihar wajen yin addu’o’in hadin kai da juriya a tsaka da kalubalen tattalin arziki da ake fama da shi, inda ya tabbatar da cewa matsalolin da ake fama da su a halin yanzu masu wucewa ne, yana mai cewa Nijeriya za ta farfaɗo daga wadannan matsaloli.

Gwamnan ya kuma bukaci al’ummar Musulmi su ci gaba da dabbaƙa ibadun da suka gudanar a cikin watan mai alfarma tare da dorar da darussan da aka koya a yayin tafsirai don ci gaban addini, da al’umma baki ɗaya, yana mai jaddada cewa Nijeriya tana matukar bukatar mutanen kirki, masu kyawawan halaye don shawo kan munanan ayyukan da wasu ‘yan tsirarun da ba sa nufin kasar da alheri suka haddasa.

Shugaban kungiyar gwamnonin na Arewa ya kuma jaddada mahimmancin kyawawan dabi’u wajen yakar matsalolin al’umma.

Ya ce, “Wannan lokaci na sallar idi yana nuni da sadaukarwa, kauna da biyayya ga rukunan Musulunci. Don haka ina yi mana wasiyya da mu dabbaƙa darussan da muka koya a wannan wata na Ramadan da nuna kauna ga juna tare da inganta zaman lafiya a tsakanin al’ummarmu daban-daban”.

“Kamar yadda dukkanmu muka tuna da marassa galihu da talakawa a cikin watan na Ramadan, ina rokonmu mu ci gaba da wadannan dabi’u har bayan Ramadan.”

Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na wanzar da zaman lafiya da tsaro, inda ya sha alwashin cewa gwamnatin ba za ta amince da duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiyan da ake mora a jihar ba.

Da yake jaddada muhimmancin samar da romon demokradiyya, ya bai wa al’ummar jihar tabbacin cewa gwamnatinsa tana mai da hankali wajen nausa jihar da al’ummarta gaba.

Gwamna Inuwa Yahaya ya ja hankalin al’ummar jihar su yi amfani da wasu tsare-tsaren da gwamnatin tarayya da ta jihar suka bullo da su don bunkasa tattalin arzikinsu.

Gombe

Ya kuma bayyana muhimmancin noma wajen bunkasa tattalin arziki da tabbatar da samar da abinci, inda ya bukaci jama’a su yi amfani da damar da za su samu a harkar noma, tare da karkata akalarsu ga sana’o’i masu nagarta, yana mai bayyana kwarin guiwarsa kan al’ummar Jihar ta Gombe.

Ya yi kira ga sarakunan gargajiya, malaman addini, da shugabannin al’umma su ci gaba da bai wa gwamnati goyon baya wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro don ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin jihar, yana mai tabbatar da aniyarsa ta aiwatar da ayyukan raya kasa da tsare-tsaren bunkasa jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Sin Za Ta Ci Gaba Da Shiga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Next Post

Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

Related

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

1 hour ago
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

3 hours ago
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa
Labarai

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

5 hours ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

5 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

17 hours ago
Next Post
Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.