• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Sallar Idi A Gombe

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Yadda Aka Gudanar Da Sallar Idi A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya tare da Sarkin Gombe, Alhaji (Dakta) Abubakar Shehu Abubakar III, gami da dubban al’ummar musulmai ne suka gudanar da Sallar Idi mai raka’a biyu a jihar da ke alamta kammala Azumin watan Ramadana.

Mataimakin babban limamin Gombe, Ustaz Aliyu Hammari, shi ne ya jagoranci Sallar wacce ta hada fuskokin dubban jama’a da jami’an gwamnati, kakakin majalisar jihar da sauransu.

  • Sakon Sallah: Gwamna Nasir Ya Yi Kira Da Hadin Kai Don Gina Jihar Kebbi
  • Gidauniyar Saraki Ta Kammala Shirin Rabon Abincin Buda-baki

Kazalika, bayan kammala Sallar Idin an gudanar da hawan sallah cikin kasaita da kyale-kyale domin nuna murna da farin ciki da wannan Idin.

A sakonsa na sallah ga al’ummar musulmai, Gwamnan Jihar Gombe, kuma Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya al’ummar Musulmin jihar murnar bikin Sallar Idi, yayin da suka bi sahun takwarorinsu na faɗin duniya don alamta ƙarshen azumin watan Ramadan mai alfarma.

A sakonsa na fatan alheri dauke da sanya hannun kakakinsa Malam Ismaila Uba Misilli, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci Musulmai su kiyaye koyarwa da dabi’un da suka koya a cikin watan na Ramadan, tare da ɗabbaƙasu a cikin rayuwarsu ta yau da kullum don ci gaban al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gombe

Ya jawo hankalin al’ummar jihar wajen yin addu’o’in hadin kai da juriya a tsaka da kalubalen tattalin arziki da ake fama da shi, inda ya tabbatar da cewa matsalolin da ake fama da su a halin yanzu masu wucewa ne, yana mai cewa Nijeriya za ta farfaɗo daga wadannan matsaloli.

Gwamnan ya kuma bukaci al’ummar Musulmi su ci gaba da dabbaƙa ibadun da suka gudanar a cikin watan mai alfarma tare da dorar da darussan da aka koya a yayin tafsirai don ci gaban addini, da al’umma baki ɗaya, yana mai jaddada cewa Nijeriya tana matukar bukatar mutanen kirki, masu kyawawan halaye don shawo kan munanan ayyukan da wasu ‘yan tsirarun da ba sa nufin kasar da alheri suka haddasa.

Shugaban kungiyar gwamnonin na Arewa ya kuma jaddada mahimmancin kyawawan dabi’u wajen yakar matsalolin al’umma.

Ya ce, “Wannan lokaci na sallar idi yana nuni da sadaukarwa, kauna da biyayya ga rukunan Musulunci. Don haka ina yi mana wasiyya da mu dabbaƙa darussan da muka koya a wannan wata na Ramadan da nuna kauna ga juna tare da inganta zaman lafiya a tsakanin al’ummarmu daban-daban”.

“Kamar yadda dukkanmu muka tuna da marassa galihu da talakawa a cikin watan na Ramadan, ina rokonmu mu ci gaba da wadannan dabi’u har bayan Ramadan.”

Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na wanzar da zaman lafiya da tsaro, inda ya sha alwashin cewa gwamnatin ba za ta amince da duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiyan da ake mora a jihar ba.

Da yake jaddada muhimmancin samar da romon demokradiyya, ya bai wa al’ummar jihar tabbacin cewa gwamnatinsa tana mai da hankali wajen nausa jihar da al’ummarta gaba.

Gwamna Inuwa Yahaya ya ja hankalin al’ummar jihar su yi amfani da wasu tsare-tsaren da gwamnatin tarayya da ta jihar suka bullo da su don bunkasa tattalin arzikinsu.

Gombe

Ya kuma bayyana muhimmancin noma wajen bunkasa tattalin arziki da tabbatar da samar da abinci, inda ya bukaci jama’a su yi amfani da damar da za su samu a harkar noma, tare da karkata akalarsu ga sana’o’i masu nagarta, yana mai bayyana kwarin guiwarsa kan al’ummar Jihar ta Gombe.

Ya yi kira ga sarakunan gargajiya, malaman addini, da shugabannin al’umma su ci gaba da bai wa gwamnati goyon baya wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro don ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin jihar, yana mai tabbatar da aniyarsa ta aiwatar da ayyukan raya kasa da tsare-tsaren bunkasa jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Sin Za Ta Ci Gaba Da Shiga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Next Post

Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

Related

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

4 hours ago
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu
Manyan Labarai

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

6 hours ago
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya
Labarai

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

12 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

22 hours ago
Next Post
Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.