ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Sallar Idi A Gombe

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya tare da Sarkin Gombe, Alhaji (Dakta) Abubakar Shehu Abubakar III, gami da dubban al’ummar musulmai ne suka gudanar da Sallar Idi mai raka’a biyu a jihar da ke alamta kammala Azumin watan Ramadana.

Mataimakin babban limamin Gombe, Ustaz Aliyu Hammari, shi ne ya jagoranci Sallar wacce ta hada fuskokin dubban jama’a da jami’an gwamnati, kakakin majalisar jihar da sauransu.

  • Sakon Sallah: Gwamna Nasir Ya Yi Kira Da Hadin Kai Don Gina Jihar Kebbi
  • Gidauniyar Saraki Ta Kammala Shirin Rabon Abincin Buda-baki

Kazalika, bayan kammala Sallar Idin an gudanar da hawan sallah cikin kasaita da kyale-kyale domin nuna murna da farin ciki da wannan Idin.

ADVERTISEMENT

A sakonsa na sallah ga al’ummar musulmai, Gwamnan Jihar Gombe, kuma Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya al’ummar Musulmin jihar murnar bikin Sallar Idi, yayin da suka bi sahun takwarorinsu na faɗin duniya don alamta ƙarshen azumin watan Ramadan mai alfarma.

A sakonsa na fatan alheri dauke da sanya hannun kakakinsa Malam Ismaila Uba Misilli, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci Musulmai su kiyaye koyarwa da dabi’un da suka koya a cikin watan na Ramadan, tare da ɗabbaƙasu a cikin rayuwarsu ta yau da kullum don ci gaban al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Gombe

Ya jawo hankalin al’ummar jihar wajen yin addu’o’in hadin kai da juriya a tsaka da kalubalen tattalin arziki da ake fama da shi, inda ya tabbatar da cewa matsalolin da ake fama da su a halin yanzu masu wucewa ne, yana mai cewa Nijeriya za ta farfaɗo daga wadannan matsaloli.

Gwamnan ya kuma bukaci al’ummar Musulmi su ci gaba da dabbaƙa ibadun da suka gudanar a cikin watan mai alfarma tare da dorar da darussan da aka koya a yayin tafsirai don ci gaban addini, da al’umma baki ɗaya, yana mai jaddada cewa Nijeriya tana matukar bukatar mutanen kirki, masu kyawawan halaye don shawo kan munanan ayyukan da wasu ‘yan tsirarun da ba sa nufin kasar da alheri suka haddasa.

Shugaban kungiyar gwamnonin na Arewa ya kuma jaddada mahimmancin kyawawan dabi’u wajen yakar matsalolin al’umma.

Ya ce, “Wannan lokaci na sallar idi yana nuni da sadaukarwa, kauna da biyayya ga rukunan Musulunci. Don haka ina yi mana wasiyya da mu dabbaƙa darussan da muka koya a wannan wata na Ramadan da nuna kauna ga juna tare da inganta zaman lafiya a tsakanin al’ummarmu daban-daban”.

“Kamar yadda dukkanmu muka tuna da marassa galihu da talakawa a cikin watan na Ramadan, ina rokonmu mu ci gaba da wadannan dabi’u har bayan Ramadan.”

Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na wanzar da zaman lafiya da tsaro, inda ya sha alwashin cewa gwamnatin ba za ta amince da duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiyan da ake mora a jihar ba.

Da yake jaddada muhimmancin samar da romon demokradiyya, ya bai wa al’ummar jihar tabbacin cewa gwamnatinsa tana mai da hankali wajen nausa jihar da al’ummarta gaba.

Gwamna Inuwa Yahaya ya ja hankalin al’ummar jihar su yi amfani da wasu tsare-tsaren da gwamnatin tarayya da ta jihar suka bullo da su don bunkasa tattalin arzikinsu.

Gombe

Ya kuma bayyana muhimmancin noma wajen bunkasa tattalin arziki da tabbatar da samar da abinci, inda ya bukaci jama’a su yi amfani da damar da za su samu a harkar noma, tare da karkata akalarsu ga sana’o’i masu nagarta, yana mai bayyana kwarin guiwarsa kan al’ummar Jihar ta Gombe.

Ya yi kira ga sarakunan gargajiya, malaman addini, da shugabannin al’umma su ci gaba da bai wa gwamnati goyon baya wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro don ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin jihar, yana mai tabbatar da aniyarsa ta aiwatar da ayyukan raya kasa da tsare-tsaren bunkasa jihar.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Next Post
Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.