• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Hawan Daba A Ƙauran Namoda Da Naɗa Gwamna Dauda Sarauta

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
Yadda Aka Gudanar Da Hawan Daba A Ƙauran Namoda Da Naɗa Gwamna Dauda Sarauta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya halarci bikin hawan Daba a Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda a ranar Lahadin nan.

Masarautar Ƙauran Namoda na gudanar da wani gagarumin biki na musamman bayan Sallar Idi, wanda aka fi sani da Hawan Durbar duk shekara.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa, bikin hawan Durbar na haɗa jama’a domin murnar zagayowar ranar sallah da kaɗe-kaɗe, raye-raye, da sauran al’adun gargajiya.

Sanarwar ta ce, a yayin bikin hawan Durbar mai ban sha’awa, an naɗa Gwamna Lawal sarautar ‘Wakilin Kaura’, wanda ke nufin wakilin wanda ya kafa masarautar.

  • Yanzu-yanzu: Hatsaniya Ta Kaure Tsakanin Sojoji Da Matasa A Gashuwa

 

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

“Gwamna Dauda Lawal ya halarci bikin hawan Daba na Masarautar Ƙauran Namoda a yau.

“Hawan Daba wani biki ne mai ban-sha’awa wanda ke nuna al’adun gargajiyar masarautar Ƙauran Namoda. Hawan Durbar da ke Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda tana bai wa jama’a damar haɗuwa waje guda, tare da taya murna zagayowar sallar wannan shekara.

“Bikin Daba na bana ya zama mai matuƙar muhimmanci ga masarautar, domin wannan ne karon farko da wani gwamna mai ci a jihar ya halarci taron.

“Gwamna Lawal, sanye da kayan gargajiya, ya shiga hawan Daba a lokacin da yake kan dokin da aka ƙawata da kayan ado.

Hawa

“A lokacin da ake gudanar da bikin, Sarkin Ƙauran Namoda, wanda aka fi sani da Sarkin Kiyawan Ƙauran Namoda, Dokta Sanusi Muhammad Ahmad Asha ya bai wa Gwamna Dauda Lawal sarautar gargajiya ta Wakilin Ƙaura, wato wakilin wanda ya kafa masarautar. Wannan karimcin ya nuna godiya ga halartar gwamnan a wajen bikin.”

Sannan Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da ƙofar birnin Modomawa, tsohuwar ƙofar Kauran Namoda tun daga 1807-1810.

Ya kuma duba cibiyar kula da gidan talabijin ta Nijeriya NTA a Ƙaramar Hukumar, inda ya yi alƙawarin bayar da duk wani tallafin da ya dace don farfaɗo da tashar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bikin SallahGwamna Dauda LawalHawan DabaJihar ZamfaraƘauran Namoda
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Kasa ne Ke Iya Magance Matsalar Tsaro Ba Gwamnoni Ba – Sanata Yari

Next Post

Bangaren Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Kasar Sin Ya Yi Kira Ga EU Da Ya Gudanar Da Bincike Bisa Adalci

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

22 minutes ago
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

51 minutes ago
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

4 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

5 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

17 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

18 hours ago
Next Post
Bangaren Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Kasar Sin Ya Yi Kira Ga EU Da Ya Gudanar Da Bincike Bisa Adalci

Bangaren Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Kasar Sin Ya Yi Kira Ga EU Da Ya Gudanar Da Bincike Bisa Adalci

LABARAI MASU NASABA

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.