• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kawo Karshen Karancin Malaman Makarantun Firamare A Nijeriya

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
A Kawo Karshen Karancin Malaman Makarantun Firamare A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayanan da aka samu a rahoto na baya-bayan nan daga Hukumar Kula da Makarantun Firamare (UBEC) yana da matukar tayar da hankali. Rahoton shekarar 2022 zuwa 2023 na kididdigar yawan Malaman firamare da ake da su ya nuna cewa, Nijeriya na fuskantar karancin malamai a matakin firamare yayin da ake da gibin Malamai fiye da Malamai 195,000 a makarantun gwamnati na fadin tarayyar kasar nan.

Karancin kwararrun Malamai a matakin farko na tsarin ilimin kasar nan abu ne da ke bukatar a dauki matakin gaggawa daga dukkan matakan gwamnati da masu ruwa da tsaki a fadin kasar nan.

  • Bangaren Amurka Ya Mayar Wa Bangaren Sin Da Kayayyakin Tarihi 38 Da Suka Bata Daga Sin
  • Sharhi: Kokarin Fahimtar Yanayin Tattalin Arzikin Sin Ta Bangarorin Ayyuka Guda 3

Rahoton ya gano rashin daidatio a tsakanin sauran matakan ilimi, inda aka gano matakin makarantun reno na kananan yara da matakin karamar sakandare JSS suna da issasun Malamai har sun yi masu yawa amma kuma a matakin makarantun firamare suna matukar fuskantar matsalar rashin Malamai, a wasu kauyuka ma zaka ga Malami daya ne ko biyu ke aiki a dukkan makarantun da ake da su duk kuwa da yawan dalibai.

Wannan rashin daidaito na yawan Malamai a matakan ilimi na kasar nan shi ne ya jefa kasar cikin matsalolin da suke tattare da ilimin yara. Rahoton ya kuma bayyana cewa, rashin issasun Malamai a matakin firamari shi ne ya haifar matsalar talauci da sauran matsalolin da ake fuskata a Nijeriya.

A ra’ayin wannan jaridar,in har ba a samu kwararrun Malamai ba masu aiki tukuru tare da basu ingantaccen ilimi a bangaren makarantun firamare ta yaya za’a samu yara masu hazaka da za su zama abin alfaharinmu a nan gaba har su zama shugabannin gobe? Fatan kasar nan na tattare da magance wannan matsalar gaba daya.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Abin takaici a nan shi ne abubuwan da suka haifar da wannan karancin Malamai a bayyane suke kuma kowa ya san su. Yawancin jihoji sun yi shekaru basu dauki sabbin Malamai ba, yayin da wasu ma’aikata ke barin aiki wasu kuma suna mutuwa amma ba a maye gurbinsu ba.

Wannan kuma na tattare da annobar barin kasa da aka fi sani da “japa” da kwararun Malamai ke yi, hakan ya sanya Malamai masu kwazo suna barin kasarnan zuwa kasashen waje don samun rayuwa ta gari abin da kuma shine ya kara haifar da matsalar da ake ciki.

Rashin kulawa da rashin kyawun ka’idojin aiki ga Malamai a Nijeriya yana kara taimakawa wajen korar kwararrun Malamai daga bangaren suna komawa wasu wuraren inda aka san mutuncin su.

Tuni shugaban kungiyar Malamai na kasa, NUT, Kwamrade Audu Titus Amba, ya nuna rashin jin dadinsa a kan lamariin, wannan kuma yana nuna irin kamarin da al’amarin ya kai ke nan.

Ya kuma bayyana cewa, ba za a iya samun ingantacen ilimi ba har sai an samu issasun Malamai a dukkan matakai na ilimi, musamman ma ganin ilimi shi ne kashin bayan ci gaban kowadanne al’umma.

Ba wai sun kasance a matsayin Malamai kawai ba ne, su masu saita yara ne tare da shiryar da su  domin su zama mutanen kirkin da za su zama shugabannin gobe.

Ba abin da za a amuince da shi ba ne a kasar da ke da yara fiye da  miliyan 12 da basu zuwa makaranta duk da kuma ana fuskantar tsananin rashin Malamai a matakin firamare.

Ta yaya za mu samar da ingantaccen ilimi da kuma rage yawan yaran da basu zuwa makaranta a Nijeriya bayan kuma muna fama da matsalar karancin malamai?

Lokacin daukar matakin da bai dace ba da daukar alkawurra marasa ma’ana ya wuce yanzu lokaci ne na daukar matakin da ya dace kai tsaye.

Abin jin dadin a nan shi ne, dama can a kwai daftarin tsarin farfado da tsarin ilimi a kasar nan, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a shekarar 2020,an shirya daftarin ne don bunkasa tare da inganta sana’ar koyarwa a Nijeriya.

Wannan ya hada da samar da albashi na musamman ga Malaman firamare da na sakandare tare da kara shekarun barin aikin su hakanan kuma an samar da alawus alawsu ga dalibai masu koyon aikin Malanta don karfafa masu shiga harkar koyarwar.

Abin takaici a na shi ne irin wannan kyawawan matakai da kudurori ba a kai ga aiwatar da su ba har zuwa yanzu wanda hakan ke ci gaba da sanya harkar koyarwa cikin halin ni ‘yasu.

Dole ne a gaggauta daukar mataki kan wannan lamarin da gaggawa, sai aiwatar da abin da ke tatatare cikin shi rahoton.Muna kira da wannan gwammantin a karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta amince da daukar muhimmin mataki wajen aiwatar da tsare-tsaren da tsohon shugaban kasa Buhari ya yi na farfado da bangaren ilimi.

Bayan haka kuma dole gwamnatocin jihohi su dauki nasu alhakin.Dole su gaggauta fara daukar sabbin Malamai don cike gurbin Malaman firamare da aka rasa musamman a yankunan karkara.

Ya kuma kamata a kara inganta ka’idar aiki da jin dadin Malamai don aikin ya zama yana da ban sha’awa ta yadda kwarrarun Malamai za su tsaya a cikin aikin ba tare da shirin tserewa zuwa kasashen waje ba.

Lokaci ya yi da gwamnati tare da hadin gwiwar dukakan masu ruwa da tsaki  su dauki matakin ganin kowanne yaro a Nijeriya ya samu damar zuwa makarannta tare da samun ilimin da ya kamata.

Nasarar yaran Nijeriya dama nasarar Nijeriyar tana tattare ne da nasarar da aka samu a wannan kokarin. In muka zuba jarin da ya kamata a bangaren ilimi za mu samar da yaran da za mu yi alfahari da su a nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane Fiye Da Miliyan 141 Sun Shiga Ko Fita Daga Kasar Sin A Rubu’in Farko Na Bana

Next Post

Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

1 day ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

2 days ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

3 days ago
Next Post
Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.