ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kawo Karshen Karancin Malaman Makarantun Firamare A Nijeriya

by Leadership Hausa
2 years ago
Malaman

Bayanan da aka samu a rahoto na baya-bayan nan daga Hukumar Kula da Makarantun Firamare (UBEC) yana da matukar tayar da hankali. Rahoton shekarar 2022 zuwa 2023 na kididdigar yawan Malaman firamare da ake da su ya nuna cewa, Nijeriya na fuskantar karancin malamai a matakin firamare yayin da ake da gibin Malamai fiye da Malamai 195,000 a makarantun gwamnati na fadin tarayyar kasar nan.

Karancin kwararrun Malamai a matakin farko na tsarin ilimin kasar nan abu ne da ke bukatar a dauki matakin gaggawa daga dukkan matakan gwamnati da masu ruwa da tsaki a fadin kasar nan.

  • Bangaren Amurka Ya Mayar Wa Bangaren Sin Da Kayayyakin Tarihi 38 Da Suka Bata Daga Sin
  • Sharhi: Kokarin Fahimtar Yanayin Tattalin Arzikin Sin Ta Bangarorin Ayyuka Guda 3

Rahoton ya gano rashin daidatio a tsakanin sauran matakan ilimi, inda aka gano matakin makarantun reno na kananan yara da matakin karamar sakandare JSS suna da issasun Malamai har sun yi masu yawa amma kuma a matakin makarantun firamare suna matukar fuskantar matsalar rashin Malamai, a wasu kauyuka ma zaka ga Malami daya ne ko biyu ke aiki a dukkan makarantun da ake da su duk kuwa da yawan dalibai.

ADVERTISEMENT

Wannan rashin daidaito na yawan Malamai a matakan ilimi na kasar nan shi ne ya jefa kasar cikin matsalolin da suke tattare da ilimin yara. Rahoton ya kuma bayyana cewa, rashin issasun Malamai a matakin firamari shi ne ya haifar matsalar talauci da sauran matsalolin da ake fuskata a Nijeriya.

A ra’ayin wannan jaridar,in har ba a samu kwararrun Malamai ba masu aiki tukuru tare da basu ingantaccen ilimi a bangaren makarantun firamare ta yaya za’a samu yara masu hazaka da za su zama abin alfaharinmu a nan gaba har su zama shugabannin gobe? Fatan kasar nan na tattare da magance wannan matsalar gaba daya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Abin takaici a nan shi ne abubuwan da suka haifar da wannan karancin Malamai a bayyane suke kuma kowa ya san su. Yawancin jihoji sun yi shekaru basu dauki sabbin Malamai ba, yayin da wasu ma’aikata ke barin aiki wasu kuma suna mutuwa amma ba a maye gurbinsu ba.

Wannan kuma na tattare da annobar barin kasa da aka fi sani da “japa” da kwararun Malamai ke yi, hakan ya sanya Malamai masu kwazo suna barin kasarnan zuwa kasashen waje don samun rayuwa ta gari abin da kuma shine ya kara haifar da matsalar da ake ciki.

Rashin kulawa da rashin kyawun ka’idojin aiki ga Malamai a Nijeriya yana kara taimakawa wajen korar kwararrun Malamai daga bangaren suna komawa wasu wuraren inda aka san mutuncin su.

Tuni shugaban kungiyar Malamai na kasa, NUT, Kwamrade Audu Titus Amba, ya nuna rashin jin dadinsa a kan lamariin, wannan kuma yana nuna irin kamarin da al’amarin ya kai ke nan.

Ya kuma bayyana cewa, ba za a iya samun ingantacen ilimi ba har sai an samu issasun Malamai a dukkan matakai na ilimi, musamman ma ganin ilimi shi ne kashin bayan ci gaban kowadanne al’umma.

Ba wai sun kasance a matsayin Malamai kawai ba ne, su masu saita yara ne tare da shiryar da su  domin su zama mutanen kirkin da za su zama shugabannin gobe.

Ba abin da za a amuince da shi ba ne a kasar da ke da yara fiye da  miliyan 12 da basu zuwa makaranta duk da kuma ana fuskantar tsananin rashin Malamai a matakin firamare.

Ta yaya za mu samar da ingantaccen ilimi da kuma rage yawan yaran da basu zuwa makaranta a Nijeriya bayan kuma muna fama da matsalar karancin malamai?

Lokacin daukar matakin da bai dace ba da daukar alkawurra marasa ma’ana ya wuce yanzu lokaci ne na daukar matakin da ya dace kai tsaye.

Abin jin dadin a nan shi ne, dama can a kwai daftarin tsarin farfado da tsarin ilimi a kasar nan, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a shekarar 2020,an shirya daftarin ne don bunkasa tare da inganta sana’ar koyarwa a Nijeriya.

Wannan ya hada da samar da albashi na musamman ga Malaman firamare da na sakandare tare da kara shekarun barin aikin su hakanan kuma an samar da alawus alawsu ga dalibai masu koyon aikin Malanta don karfafa masu shiga harkar koyarwar.

Abin takaici a na shi ne irin wannan kyawawan matakai da kudurori ba a kai ga aiwatar da su ba har zuwa yanzu wanda hakan ke ci gaba da sanya harkar koyarwa cikin halin ni ‘yasu.

Dole ne a gaggauta daukar mataki kan wannan lamarin da gaggawa, sai aiwatar da abin da ke tatatare cikin shi rahoton.Muna kira da wannan gwammantin a karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta amince da daukar muhimmin mataki wajen aiwatar da tsare-tsaren da tsohon shugaban kasa Buhari ya yi na farfado da bangaren ilimi.

Bayan haka kuma dole gwamnatocin jihohi su dauki nasu alhakin.Dole su gaggauta fara daukar sabbin Malamai don cike gurbin Malaman firamare da aka rasa musamman a yankunan karkara.

Ya kuma kamata a kara inganta ka’idar aiki da jin dadin Malamai don aikin ya zama yana da ban sha’awa ta yadda kwarrarun Malamai za su tsaya a cikin aikin ba tare da shirin tserewa zuwa kasashen waje ba.

Lokaci ya yi da gwamnati tare da hadin gwiwar dukakan masu ruwa da tsaki  su dauki matakin ganin kowanne yaro a Nijeriya ya samu damar zuwa makarannta tare da samun ilimin da ya kamata.

Nasarar yaran Nijeriya dama nasarar Nijeriyar tana tattare ne da nasarar da aka samu a wannan kokarin. In muka zuba jarin da ya kamata a bangaren ilimi za mu samar da yaran da za mu yi alfahari da su a nan gaba.

Malaman
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.