• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Cafke ‘Yan Kwaya 50,901 Da Gurfanar Da 9,034 A Shekara 3 – Marwa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Mun Cafke ‘Yan Kwaya 50,901 Da Gurfanar Da 9,034 A Shekara 3 – Marwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Shugaban hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA), Mohamed Buba Marwa ya bayyana cewa sun samu nasarar cafke ‘yan kwaya guda 50,901 da suka kasance masu aikata laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi tare da samu nasarar gurfanarwa da daure mutum 9,034 hadi da kamo sama da tan-tan 7,561 na haramtattun kwayoyi a cikin watanni 38 da suka wuce.

A cikin shekaru uku kuma, hukumar ta lalata da tarwatsa hekta 1,057.33348 na tabar wiwi a sassa daban-daban na Nijeriya a wani mataki na nuna aikin ba sani ba sabo kan yaki da miyagun kwayoyi da safararsu.

  • Nijeriya Da Jamhoriyyar Benin Za Su Hada Kai Don Inganta Harkokin Kasuwanci
  • Nijeriya Da Jamhoriyyar Benin Za Su Hada Kai Don Inganta Harkokin Kasuwanci

Sannan a cewarsa, wannan wani kyakkyawar sako ne ga masu mu’amala da miyagun kwayoyi da su gane cewa Nijeriya a yanzu ba za ta lamunci munanan ayyukansu ba.

Marwa ya shaida haka ne a ranar Litinin a Legas yayin da ke jawabi wajen kaddamar da mika ofishin da Gwamnatin Burtaniya ta gina domin agaza wa kokarin hukumar NDLEA na cigaba da yaki da masu mu’amala da miyagun kwayoyi da dakile safaran miyagun kwayoyi a Nijeriya.

A cewarsa, “Mun hadu a nan ne ba kawai domin mu kaddamar da sabon ginin ofishi ba, har ma da mu yi murna kan irin nasarorin da muka cimma kan yaki da muke yi da masu ta’anmuli da miyagun kwayoyi da safararsa. A yau, da wannan kaddamar da sabon ofishin da gwamnatin Burtaniya ta yi da nufin karfafa wa kokarinmu wajen ci gaba da dakile amfani da miyagun kwayoyi.

“Dole ne na jinjina da mika godiyarmu ga gwamnatin Burtaniya bisa wannan gagarumin gudunmawa da ta mana. Kuma, da kyakkyawar hadin guiwa da ke tsakani za mu samu nasarar ci gaba da dakile ayyukan ‘yan ta’adda da tsarkake Nijeriya daga ta’anmuli da miyagun kwayoyi hadi da jigilarsu.

“Wannan ofishin aikin ba kawai an gina domin gudanar da aiki zalla ba ne, zai kuma kyautata dangantaka a tsakanin kasashen biyu wajen ci gaba da yaki da safaran miyagun kwayoyi.”

A cewarsa, alfanun da sabon ofishin zai musu na da matukar yawa da suka hada da bincike, bibiya da kuma sanya ido kan miyagun kwayoyi da ake jigilarsu domin dakile aniyar masu mu’amala da su.

“Mun kama kilogiram 7,560,748.5 (Tan 7,561), ba kawai dakile miyagun kwayoyi ba ne har ma da toshe wa masu jigilar aniyarsu na rabawa a inda suke son rarrabawa. Mun kuma samu nasarar tarwatsa hekta 1,057.33348 na gonar tabar wiwi a cikin shekaru uku da suka wuce,” ya shaida.

Duk da kyautar ofishin, shugaban hukumar ya kuma sake neman hadin guiwar gwamnatin Burtaniya domin kara kyautata himma wajen yaki da matsalar sha da fataucin miyagun kwayoyi a tsakanin kasashen biyu.

A cewarsa, ba za su bari a yi sako-sako da wadanan nasarorin da suke samu ba, ya nemi jami’ansa da su kara himma wajen shiga lungu da sako domin dakile aniyar masu sha da fataucin miyagun kwayoyi.

Da yake jawabinsa a wajen taron, mataimakin wakilin Burtaniya a Nijeriya, Jonny Badter, ya ba da tabbacin gwamnatin kasarsu na ci gaba da taimaka wa NDLEA da Nijeriya a bangarorin yaki da fataucin miyagun kwayoyi da sauran muhimman bangarori.

Ya kuma nuna farin cikin gwamnatin Burtaniya kan yadda NDLEA ke samun gagarumin nasara wajen yaki da masu sha da masu fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya, ya ce kofarsu a bude take wajen ci gaba da taimaka wa Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Lalacewar Babbar Tashar Lantarki Ta Addabi ‘Yan Nijeriya

Next Post

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Related

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

4 minutes ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 hour ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

6 hours ago
Kwaya
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

7 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kwaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.