ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Cafke ‘Yan Kwaya 50,901 Da Gurfanar Da 9,034 A Shekara 3 – Marwa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Kwaya

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Shugaban hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA), Mohamed Buba Marwa ya bayyana cewa sun samu nasarar cafke ‘yan kwaya guda 50,901 da suka kasance masu aikata laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi tare da samu nasarar gurfanarwa da daure mutum 9,034 hadi da kamo sama da tan-tan 7,561 na haramtattun kwayoyi a cikin watanni 38 da suka wuce.

A cikin shekaru uku kuma, hukumar ta lalata da tarwatsa hekta 1,057.33348 na tabar wiwi a sassa daban-daban na Nijeriya a wani mataki na nuna aikin ba sani ba sabo kan yaki da miyagun kwayoyi da safararsu.

  • Nijeriya Da Jamhoriyyar Benin Za Su Hada Kai Don Inganta Harkokin Kasuwanci
  • Nijeriya Da Jamhoriyyar Benin Za Su Hada Kai Don Inganta Harkokin Kasuwanci

Sannan a cewarsa, wannan wani kyakkyawar sako ne ga masu mu’amala da miyagun kwayoyi da su gane cewa Nijeriya a yanzu ba za ta lamunci munanan ayyukansu ba.

Marwa ya shaida haka ne a ranar Litinin a Legas yayin da ke jawabi wajen kaddamar da mika ofishin da Gwamnatin Burtaniya ta gina domin agaza wa kokarin hukumar NDLEA na cigaba da yaki da masu mu’amala da miyagun kwayoyi da dakile safaran miyagun kwayoyi a Nijeriya.

A cewarsa, “Mun hadu a nan ne ba kawai domin mu kaddamar da sabon ginin ofishi ba, har ma da mu yi murna kan irin nasarorin da muka cimma kan yaki da muke yi da masu ta’anmuli da miyagun kwayoyi da safararsa. A yau, da wannan kaddamar da sabon ofishin da gwamnatin Burtaniya ta yi da nufin karfafa wa kokarinmu wajen ci gaba da dakile amfani da miyagun kwayoyi.

“Dole ne na jinjina da mika godiyarmu ga gwamnatin Burtaniya bisa wannan gagarumin gudunmawa da ta mana. Kuma, da kyakkyawar hadin guiwa da ke tsakani za mu samu nasarar ci gaba da dakile ayyukan ‘yan ta’adda da tsarkake Nijeriya daga ta’anmuli da miyagun kwayoyi hadi da jigilarsu.

“Wannan ofishin aikin ba kawai an gina domin gudanar da aiki zalla ba ne, zai kuma kyautata dangantaka a tsakanin kasashen biyu wajen ci gaba da yaki da safaran miyagun kwayoyi.”

A cewarsa, alfanun da sabon ofishin zai musu na da matukar yawa da suka hada da bincike, bibiya da kuma sanya ido kan miyagun kwayoyi da ake jigilarsu domin dakile aniyar masu mu’amala da su.

“Mun kama kilogiram 7,560,748.5 (Tan 7,561), ba kawai dakile miyagun kwayoyi ba ne har ma da toshe wa masu jigilar aniyarsu na rabawa a inda suke son rarrabawa. Mun kuma samu nasarar tarwatsa hekta 1,057.33348 na gonar tabar wiwi a cikin shekaru uku da suka wuce,” ya shaida.

Duk da kyautar ofishin, shugaban hukumar ya kuma sake neman hadin guiwar gwamnatin Burtaniya domin kara kyautata himma wajen yaki da matsalar sha da fataucin miyagun kwayoyi a tsakanin kasashen biyu.

A cewarsa, ba za su bari a yi sako-sako da wadanan nasarorin da suke samu ba, ya nemi jami’ansa da su kara himma wajen shiga lungu da sako domin dakile aniyar masu sha da fataucin miyagun kwayoyi.

Da yake jawabinsa a wajen taron, mataimakin wakilin Burtaniya a Nijeriya, Jonny Badter, ya ba da tabbacin gwamnatin kasarsu na ci gaba da taimaka wa NDLEA da Nijeriya a bangarorin yaki da fataucin miyagun kwayoyi da sauran muhimman bangarori.

Ya kuma nuna farin cikin gwamnatin Burtaniya kan yadda NDLEA ke samun gagarumin nasara wajen yaki da masu sha da masu fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya, ya ce kofarsu a bude take wajen ci gaba da taimaka wa Nijeriya.

Kwaya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.