• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da karuwar darajar naira, tsadar farashin kayayyaki ta ci gaba da lulawa sama a Nijeriya. A yanzu dai ana sayar da kowacce dalar Amurka guda daya kan naira 1 a kasuwannin bayan fage.

A cewar hukumomi, wannan matakin ci gaba ne kuma tagomashi ne da naira ke samu a kan dala, sai dai duk da wannan matakin, tsadar kayan masarufi bai ragu ba, illa ma karuwa da ya yi.

  • Jihar Benuwai Ta Bankado Mutum 35 Masu Yi Wa Sirin Tattara Harajinta Zagon-Kasa
  • Nijeriya Da Jamhoriyyar Benin Za Su Hada Kai Don Inganta Harkokin Kasuwanci

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar kiddiga ta kasa (NBS) ta ce farashin kayan masarufi ya sake yin tashin gwauron zabi da kaso 33.20 a cikin 100 a watan Maris din 2024, idan aka kwatanta da kaso 31.70 cikin 100 a watan Fabrairu.

Ci gaban tagomashin da aka samu a kan darajar naira kan dalar Amurka ya samu ne tun a ranar 26 ga watan Satumban 2023.

A cikin shekara guda an samu karuwar hauhawar farashi da kaso 11.16, idan aka kwatanta da kaso 22.04 cikin dari a watan Maris din 2023.

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

A cewar rahoton, tashin farashin kayan abinci ya haura da kaso 40.01 a cikin shekara guda a watan Maris, sama da kaso 15.56 cikin dari da aka samu kari domin a watan Maris na 2023 farashin na kaso 24.45.

Kayan da suka tashin sun hada da na farashin makamashi zuwa kaso 25.90 cikin dari a watan Maris, inda ya karu da kaso 6.26 sabanin kaso 19.63 da aka samu a watan Maris na 2023.

Hukumar NBS ta ce tashin farashin kayan abinci ya samu asali ne sakamakon karuwar farashin gari, gero buredi da nau’ikan hatsi, doya, dawa, da kuma busasshen kifi.

Sauran abubuwan da suka janyo tashin farashin kayan abincin sun kuma kunshi mangyade, nama, hanta, madara, bombita, ruwan lelon da dai sauransu.

Bugu da kari, tsadar kudin sufuri da zirga-zirga su ma sun kara ba da gudunmawa wajen tashin farashin kayan masarufi a Nijeriya, kamar yadda rahoton hukumar NBS ta tabbatar.

Tambayen da Nijeriya suke ci gaba da yi shi ne, me ya sa farashin kayayyaki ba su sauko kasa ba? Domin a baya ana cewa tashin farashin dala ne ya haifar da tsadar kayayyaki.

Wasu daga cikin ‘yan kasuwa sun bayyana cewa saukar farashin dal aba zai iya sauko da farashin kayayyaki nan take ba, domin mafi yawancinsu suna tare da tsofaffin kayayyaki ne wanda suka siyo a lokacin tsadar farashin dala, sai sun iya sayar da wadannan kayayyaki ne kafin za su sayo sabbin kaya a farashi mai rahusa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Cafke ‘Yan Kwaya 50,901 Da Gurfanar Da 9,034 A Shekara 3 – Marwa

Next Post

Gwamnatin Tarayya Na Da laifin Kan Hauhawar Farashin Abinci – Marafan Gonin Gora

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

5 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da ÆŠansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

8 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

9 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

11 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

12 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Da laifin Kan Hauhawar Farashin Abinci – Marafan Gonin Gora

Gwamnatin Tarayya Na Da laifin Kan Hauhawar Farashin Abinci - Marafan Gonin Gora

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.