• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Da Suka Dabaibaye Sabbin Jami’o’i

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Ilimi
0
Matsalolin Da Suka Dabaibaye Sabbin Jami’o’i
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda alkalumma suka nuna daga Hukumar Kula da Al’amuran Jami’o’i ta Kasa, akwai jami’o’i 10 na gwamnatin tarayya, da 22 na Jihohi, sai kuma 58 na masu zaman kansu da aka kirkiro tun daga 2015 zuwa yanzu.

Wasu na ganin wannan wata dama ce ta samun ilimin jami’a, da suke da zabin wadda za su tafi, yayin da wasu kuma na ganin ya dace ya dace a samar masu da duk abubuwan da suke bukata domin ba dalibai su samu ingantaccen ilimi ba ma kamar Jami’oin Jihohi da na gwamnatin tarayya.

  • Kotu Ta Tsare Mutane 29 Masu Rajin Kafa Kasar Yarbawa A Oyo
  • Mun Ceto Sama Da Mutane 1000 Ba Tare Da Biyan Kudin Fansa Ba – Ribadu

Abin bai ma tsaya kan kudaden da za a tafiyar da jami’o’in ba. Masu fashin baki sun ce har ma akwai sauran matsaloli musamman ma ta bangaren kwararrun malamai da suma za su zama suna da dukkan abubuwan da sauran Jami’o’in duniya ke da su.

Daya daga abubuwan da ke kawo koma-baya ga irin sabbin jami’o’in shi ne, irin Ilimin da suka samu a jami’o’in tamkar koma-baya ne ga sauran Jami’o’in da aka kafa kafin su, yadda ake tsammanin wadanda suka kammala Jami’o’i akwai banbanci mai nisa tsakaninsu.

Ba tare da isassun kudade ba, lamarin fasaha, da samun taimako, yawancin Jami’o’i masu zaman kansu suna ta kokarin yadda za su ci gaba da kasancewa a matsayinsu, zai yi wuya su samar da ingantaccen Ilimi wanda dalibai suke sa ran samu domin abin nasu aiki ne ja.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

Binciken da Jaridar Guardian ta yi ya nuna cewa bayan rashin kudade yawancin jami’o’in ba su da dalibai da yawa, ba abubuwan da za su taimaka wajen koyarwar, domin babu kwararrun malaman da za su koyar.

Bamidele ya ce a Jami’ar Ilimi, Kimiyya da Fasaha ta Olumilua Jihar Ekiti, dalibai suna kokari ne wajen taimaka wa kansu wajen samun ilimi tun da jami’ar ba ta da isassun abubuwan da za su taimaka wajen samun ingantaccen Ilimin, sai kuma wani babban lamari shi ne irin yanayin da suke ciki bai dace a ce an kawo batun ilimi ba.

Da yake asalinta Jami’ar Kwalejin Ilimi ce aka daga darajarta zuwa Jami’a a shekarar 2020, abubuwan da aka gada na abin da suka shafi kayayyakin aiki ba za su wadatar ba.

Daliban sun bayyana cewa suna daukar darussa ne a dakunan lacca cikin matsi da takura domin suna da yawa ta yadda wurin ba zai iya daukar su baki daya ba.

A daya bangaren kuma malamai suna zaune ne a gidajen da ba su kamata su zauna a cikinsu ba.

Wannan duk lokacin a matsayin Kwalejin Ilimi ne babu wani abin yabo da za a fada idan ana maganar abubuwan da suke taimaka wa samar da Ilimi da za a zo a gani da suka shafi abubuwan more rayuwa, babu wurin koyon da ya amsa sunansa, babu daukar nauyin zuwa tarurruka na malamai, horar da ma’aikata da ci gabansu, ga batun bunkasa dakin karatu.

Jami’in Yada Labarai na Jami’ar Temitope Akinbisoye, ya ce babbar matsalar da take damunsu ita ce rashin kudade tafiyar da  harkokinta.

“Akwai abubuwan da muke son yi amma kowane lokaci gwamnati tana ce mana kamata ya yi mu nemi wata hanya, mu kuma hanyar samun kudadenmu ba ta wuce daukar daliban da muke yi ba wajen ba su gurbin karatu.

Duk da haka kamar yadda ya kara bayani shekara uku da suka wuce lokacin da aka mai da Kwalejin zuwa Jami’a an samu ci gaba domin kuwa an ba wa dalibai 9000 guraben karatu.

A Jihar Oyo ma, lamarin duk daya ne saboda sabbin  makarantu suna ta neman yadda za su ci gaba da zama a sunansu daga cikinsu akwai Jami’ar Kola Daisi Ibadan, (KDU-I), Jami’ar Precious

Cornerstone (PCU) Ibadan, Jami’ar Atiba Oyo; Jami’ar Dominion Ibadan, Jami’ar Dominican Samonda Ibadan, da dai sauransu.

Jami’o’in tuni suka fara aiki sai dai babbar matsalar da suke fuskanta rashin isassun kudaden da za su tafiyar da ayyukansu.

Matsalar kudi na ci wa Jami’oi tuwo a kwarya abin da ya hada da daukar ma’aikata da samar musu dukkan abubuwan da za su taimake su wajen gudanar da aikinsu na koyarwa da koyo, da kuma yin bincike wajen yin hakan.

Wata ganawa da aka yi da shi ba da jimawa ba, mataimakin Shugaban Jami’ar PCU, Farfesa Kola Oloke, kira ya yi ga Hukumar Kula da Ilimin Manyan Makarantu (TETFund) da ta rika sa makarantu masu zaman kansu cikin irin taimakon da take ba sauran Jami’o’i mallakar gwamnati.

Ita kuma Jami’ar KDU-I tana da fiye da dalibai 1000 masu karau a sassa daban-daban na Jami’ar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sri Lanka Na Mutuntawa Da Amincewa Da Kasar Sin, In Ji Firaministan kasar

Next Post

Ofishin MDD Da Na Jakadancin Sin A Kenya Sun Gudanar Da Bikin Ranar Harshen Sinanci Ta MDD

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

7 days ago
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Ilimi

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

1 week ago
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
Ilimi

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

1 week ago
Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu
Ilimi

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

2 weeks ago
Next Post
Ofishin MDD Da Na Jakadancin Sin A Kenya Sun Gudanar Da Bikin Ranar Harshen Sinanci Ta MDD

Ofishin MDD Da Na Jakadancin Sin A Kenya Sun Gudanar Da Bikin Ranar Harshen Sinanci Ta MDD

LABARAI MASU NASABA

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.