ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Da Suka Dabaibaye Sabbin Jami’o’i

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Jami'o'i

Kamar yadda alkalumma suka nuna daga Hukumar Kula da Al’amuran Jami’o’i ta Kasa, akwai jami’o’i 10 na gwamnatin tarayya, da 22 na Jihohi, sai kuma 58 na masu zaman kansu da aka kirkiro tun daga 2015 zuwa yanzu.

Wasu na ganin wannan wata dama ce ta samun ilimin jami’a, da suke da zabin wadda za su tafi, yayin da wasu kuma na ganin ya dace ya dace a samar masu da duk abubuwan da suke bukata domin ba dalibai su samu ingantaccen ilimi ba ma kamar Jami’oin Jihohi da na gwamnatin tarayya.

  • Kotu Ta Tsare Mutane 29 Masu Rajin Kafa Kasar Yarbawa A Oyo
  • Mun Ceto Sama Da Mutane 1000 Ba Tare Da Biyan Kudin Fansa Ba – Ribadu

Abin bai ma tsaya kan kudaden da za a tafiyar da jami’o’in ba. Masu fashin baki sun ce har ma akwai sauran matsaloli musamman ma ta bangaren kwararrun malamai da suma za su zama suna da dukkan abubuwan da sauran Jami’o’in duniya ke da su.

ADVERTISEMENT

Daya daga abubuwan da ke kawo koma-baya ga irin sabbin jami’o’in shi ne, irin Ilimin da suka samu a jami’o’in tamkar koma-baya ne ga sauran Jami’o’in da aka kafa kafin su, yadda ake tsammanin wadanda suka kammala Jami’o’i akwai banbanci mai nisa tsakaninsu.

Ba tare da isassun kudade ba, lamarin fasaha, da samun taimako, yawancin Jami’o’i masu zaman kansu suna ta kokarin yadda za su ci gaba da kasancewa a matsayinsu, zai yi wuya su samar da ingantaccen Ilimi wanda dalibai suke sa ran samu domin abin nasu aiki ne ja.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Binciken da Jaridar Guardian ta yi ya nuna cewa bayan rashin kudade yawancin jami’o’in ba su da dalibai da yawa, ba abubuwan da za su taimaka wajen koyarwar, domin babu kwararrun malaman da za su koyar.

Bamidele ya ce a Jami’ar Ilimi, Kimiyya da Fasaha ta Olumilua Jihar Ekiti, dalibai suna kokari ne wajen taimaka wa kansu wajen samun ilimi tun da jami’ar ba ta da isassun abubuwan da za su taimaka wajen samun ingantaccen Ilimin, sai kuma wani babban lamari shi ne irin yanayin da suke ciki bai dace a ce an kawo batun ilimi ba.

Da yake asalinta Jami’ar Kwalejin Ilimi ce aka daga darajarta zuwa Jami’a a shekarar 2020, abubuwan da aka gada na abin da suka shafi kayayyakin aiki ba za su wadatar ba.

Daliban sun bayyana cewa suna daukar darussa ne a dakunan lacca cikin matsi da takura domin suna da yawa ta yadda wurin ba zai iya daukar su baki daya ba.

A daya bangaren kuma malamai suna zaune ne a gidajen da ba su kamata su zauna a cikinsu ba.

Wannan duk lokacin a matsayin Kwalejin Ilimi ne babu wani abin yabo da za a fada idan ana maganar abubuwan da suke taimaka wa samar da Ilimi da za a zo a gani da suka shafi abubuwan more rayuwa, babu wurin koyon da ya amsa sunansa, babu daukar nauyin zuwa tarurruka na malamai, horar da ma’aikata da ci gabansu, ga batun bunkasa dakin karatu.

Jami’in Yada Labarai na Jami’ar Temitope Akinbisoye, ya ce babbar matsalar da take damunsu ita ce rashin kudade tafiyar da  harkokinta.

“Akwai abubuwan da muke son yi amma kowane lokaci gwamnati tana ce mana kamata ya yi mu nemi wata hanya, mu kuma hanyar samun kudadenmu ba ta wuce daukar daliban da muke yi ba wajen ba su gurbin karatu.

Duk da haka kamar yadda ya kara bayani shekara uku da suka wuce lokacin da aka mai da Kwalejin zuwa Jami’a an samu ci gaba domin kuwa an ba wa dalibai 9000 guraben karatu.

A Jihar Oyo ma, lamarin duk daya ne saboda sabbin  makarantu suna ta neman yadda za su ci gaba da zama a sunansu daga cikinsu akwai Jami’ar Kola Daisi Ibadan, (KDU-I), Jami’ar Precious

Cornerstone (PCU) Ibadan, Jami’ar Atiba Oyo; Jami’ar Dominion Ibadan, Jami’ar Dominican Samonda Ibadan, da dai sauransu.

Jami’o’in tuni suka fara aiki sai dai babbar matsalar da suke fuskanta rashin isassun kudaden da za su tafiyar da ayyukansu.

Matsalar kudi na ci wa Jami’oi tuwo a kwarya abin da ya hada da daukar ma’aikata da samar musu dukkan abubuwan da za su taimake su wajen gudanar da aikinsu na koyarwa da koyo, da kuma yin bincike wajen yin hakan.

Wata ganawa da aka yi da shi ba da jimawa ba, mataimakin Shugaban Jami’ar PCU, Farfesa Kola Oloke, kira ya yi ga Hukumar Kula da Ilimin Manyan Makarantu (TETFund) da ta rika sa makarantu masu zaman kansu cikin irin taimakon da take ba sauran Jami’o’i mallakar gwamnati.

Ita kuma Jami’ar KDU-I tana da fiye da dalibai 1000 masu karau a sassa daban-daban na Jami’ar.

Jami'o'i
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Jihohi Suka Fara Ɗanɗana Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    ‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

MASU ALAKA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
Ofishin MDD Da Na Jakadancin Sin A Kenya Sun Gudanar Da Bikin Ranar Harshen Sinanci Ta MDD

Ofishin MDD Da Na Jakadancin Sin A Kenya Sun Gudanar Da Bikin Ranar Harshen Sinanci Ta MDD

LABARAI MASU NASABA

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026
Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026
‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

July 9, 2026
Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026
An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

July 9, 2026
kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.