ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Da Suka Dabaibaye Sabbin Jami’o’i

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Jami'o'i

Kamar yadda alkalumma suka nuna daga Hukumar Kula da Al’amuran Jami’o’i ta Kasa, akwai jami’o’i 10 na gwamnatin tarayya, da 22 na Jihohi, sai kuma 58 na masu zaman kansu da aka kirkiro tun daga 2015 zuwa yanzu.

Wasu na ganin wannan wata dama ce ta samun ilimin jami’a, da suke da zabin wadda za su tafi, yayin da wasu kuma na ganin ya dace ya dace a samar masu da duk abubuwan da suke bukata domin ba dalibai su samu ingantaccen ilimi ba ma kamar Jami’oin Jihohi da na gwamnatin tarayya.

  • Kotu Ta Tsare Mutane 29 Masu Rajin Kafa Kasar Yarbawa A Oyo
  • Mun Ceto Sama Da Mutane 1000 Ba Tare Da Biyan Kudin Fansa Ba – Ribadu

Abin bai ma tsaya kan kudaden da za a tafiyar da jami’o’in ba. Masu fashin baki sun ce har ma akwai sauran matsaloli musamman ma ta bangaren kwararrun malamai da suma za su zama suna da dukkan abubuwan da sauran Jami’o’in duniya ke da su.

ADVERTISEMENT

Daya daga abubuwan da ke kawo koma-baya ga irin sabbin jami’o’in shi ne, irin Ilimin da suka samu a jami’o’in tamkar koma-baya ne ga sauran Jami’o’in da aka kafa kafin su, yadda ake tsammanin wadanda suka kammala Jami’o’i akwai banbanci mai nisa tsakaninsu.

Ba tare da isassun kudade ba, lamarin fasaha, da samun taimako, yawancin Jami’o’i masu zaman kansu suna ta kokarin yadda za su ci gaba da kasancewa a matsayinsu, zai yi wuya su samar da ingantaccen Ilimi wanda dalibai suke sa ran samu domin abin nasu aiki ne ja.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Binciken da Jaridar Guardian ta yi ya nuna cewa bayan rashin kudade yawancin jami’o’in ba su da dalibai da yawa, ba abubuwan da za su taimaka wajen koyarwar, domin babu kwararrun malaman da za su koyar.

Bamidele ya ce a Jami’ar Ilimi, Kimiyya da Fasaha ta Olumilua Jihar Ekiti, dalibai suna kokari ne wajen taimaka wa kansu wajen samun ilimi tun da jami’ar ba ta da isassun abubuwan da za su taimaka wajen samun ingantaccen Ilimin, sai kuma wani babban lamari shi ne irin yanayin da suke ciki bai dace a ce an kawo batun ilimi ba.

Da yake asalinta Jami’ar Kwalejin Ilimi ce aka daga darajarta zuwa Jami’a a shekarar 2020, abubuwan da aka gada na abin da suka shafi kayayyakin aiki ba za su wadatar ba.

Daliban sun bayyana cewa suna daukar darussa ne a dakunan lacca cikin matsi da takura domin suna da yawa ta yadda wurin ba zai iya daukar su baki daya ba.

A daya bangaren kuma malamai suna zaune ne a gidajen da ba su kamata su zauna a cikinsu ba.

Wannan duk lokacin a matsayin Kwalejin Ilimi ne babu wani abin yabo da za a fada idan ana maganar abubuwan da suke taimaka wa samar da Ilimi da za a zo a gani da suka shafi abubuwan more rayuwa, babu wurin koyon da ya amsa sunansa, babu daukar nauyin zuwa tarurruka na malamai, horar da ma’aikata da ci gabansu, ga batun bunkasa dakin karatu.

Jami’in Yada Labarai na Jami’ar Temitope Akinbisoye, ya ce babbar matsalar da take damunsu ita ce rashin kudade tafiyar da  harkokinta.

“Akwai abubuwan da muke son yi amma kowane lokaci gwamnati tana ce mana kamata ya yi mu nemi wata hanya, mu kuma hanyar samun kudadenmu ba ta wuce daukar daliban da muke yi ba wajen ba su gurbin karatu.

Duk da haka kamar yadda ya kara bayani shekara uku da suka wuce lokacin da aka mai da Kwalejin zuwa Jami’a an samu ci gaba domin kuwa an ba wa dalibai 9000 guraben karatu.

A Jihar Oyo ma, lamarin duk daya ne saboda sabbin  makarantu suna ta neman yadda za su ci gaba da zama a sunansu daga cikinsu akwai Jami’ar Kola Daisi Ibadan, (KDU-I), Jami’ar Precious

Cornerstone (PCU) Ibadan, Jami’ar Atiba Oyo; Jami’ar Dominion Ibadan, Jami’ar Dominican Samonda Ibadan, da dai sauransu.

Jami’o’in tuni suka fara aiki sai dai babbar matsalar da suke fuskanta rashin isassun kudaden da za su tafiyar da ayyukansu.

Matsalar kudi na ci wa Jami’oi tuwo a kwarya abin da ya hada da daukar ma’aikata da samar musu dukkan abubuwan da za su taimake su wajen gudanar da aikinsu na koyarwa da koyo, da kuma yin bincike wajen yin hakan.

Wata ganawa da aka yi da shi ba da jimawa ba, mataimakin Shugaban Jami’ar PCU, Farfesa Kola Oloke, kira ya yi ga Hukumar Kula da Ilimin Manyan Makarantu (TETFund) da ta rika sa makarantu masu zaman kansu cikin irin taimakon da take ba sauran Jami’o’i mallakar gwamnati.

Ita kuma Jami’ar KDU-I tana da fiye da dalibai 1000 masu karau a sassa daban-daban na Jami’ar.

Jami'o'i
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Ofishin MDD Da Na Jakadancin Sin A Kenya Sun Gudanar Da Bikin Ranar Harshen Sinanci Ta MDD

Ofishin MDD Da Na Jakadancin Sin A Kenya Sun Gudanar Da Bikin Ranar Harshen Sinanci Ta MDD

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.