• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Ceto Mutane 7 Da Aka Sace A Sakkwato 

by Sadiq
2 years ago
DSS

Rundunar ‘yansandan farin kaya (DSS) a Jihar Sakkwato, ta mika wasu mutane bakwai da ta ceto ga gwamnatin jihar, kasa da sa’o’i 24 da sace su.

Da yake bayyana yadda aka kubutar da wadanda lamarin ya shafa, daraktan DSS a jihar, Abdulfatah Olawuno, ya ce sun samu labarin sace mutanen da ‘yan bindiga suka yi a kauyen Gundungul.

  • Shugaban Kasar Suriname: Tunanin Shugaba Xi Jinping Ya Samar Da Sabuwar Hanyar Bunkasa Duniya
  • PDP Ta Lashi Takobin Warware Rikicin Shugabancinta A Watan Agusta

“A yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa kauyen Gundungul, jami’an DSS sun yi artabu da ‘yan bindigar.

“Tun da farko ‘yan bindigar sun kashe mutane biyu a kauyen Gundungul kafin su yi awon gaba da mutanen da aka ceto.

“Dukkanin mutanen bakwai da aka ceto DSS ta gwada lafiyarsu, kafin mika su ga gwamnatin jihar,” in ji Olawuno.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Ya kara tabbatar da shirin hukumar na tabbatar da tsaro tare da neman goyon bayan al’ummar Jihar Sakkwato.

Da yake karbar wadanda aka ceto a madadin gwamnatin jihar, sakataren gwamnatin jihar, Muhammad Bello Sifawa, ya yaba wa DSS bisa bajintar da suka yi na ceto mutanen.

Ya kuma tabbatar wa da hukumomin tsaro a jihar cewa gwamnatin jihar na ci gaba da bayar da goyon baya don tabbatar da tsaro a jihar.

“Mun yaba wa DSS kan wannan aiki kuma a matsayinmu na gwamnati mai kishin kasa, za mu ci gaba da tallafa wa ma’aikata da sauran jami’an tsaro domin su gudanar da ayyukansu,” in ji Sifawa.

Sakataren ya kuma sanar da tallafin Naira 100,000 da gwamnatin jihar ta bai wa kowane daga cikin wadanda aka ceto daga hannun ‘yan bindigar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Next Post
Kwamishinan ‘Yansandan Zamfara Ya Bayar Da Cek Na Sama Da Miliyan 50 Ga Iyalan ‘Yansandan Da Suka Rasu

Kwamishinan ‘Yansandan Zamfara Ya Bayar Da Cek Na Sama Da Miliyan 50 Ga Iyalan ‘Yansandan Da Suka Rasu

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.