ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Ceto Mutane 7 Da Aka Sace A Sakkwato 

by Sadiq
2 years ago
DSS

Rundunar ‘yansandan farin kaya (DSS) a Jihar Sakkwato, ta mika wasu mutane bakwai da ta ceto ga gwamnatin jihar, kasa da sa’o’i 24 da sace su.

Da yake bayyana yadda aka kubutar da wadanda lamarin ya shafa, daraktan DSS a jihar, Abdulfatah Olawuno, ya ce sun samu labarin sace mutanen da ‘yan bindiga suka yi a kauyen Gundungul.

  • Shugaban Kasar Suriname: Tunanin Shugaba Xi Jinping Ya Samar Da Sabuwar Hanyar Bunkasa Duniya
  • PDP Ta Lashi Takobin Warware Rikicin Shugabancinta A Watan Agusta

“A yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa kauyen Gundungul, jami’an DSS sun yi artabu da ‘yan bindigar.

ADVERTISEMENT

“Tun da farko ‘yan bindigar sun kashe mutane biyu a kauyen Gundungul kafin su yi awon gaba da mutanen da aka ceto.

“Dukkanin mutanen bakwai da aka ceto DSS ta gwada lafiyarsu, kafin mika su ga gwamnatin jihar,” in ji Olawuno.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Ya kara tabbatar da shirin hukumar na tabbatar da tsaro tare da neman goyon bayan al’ummar Jihar Sakkwato.

Da yake karbar wadanda aka ceto a madadin gwamnatin jihar, sakataren gwamnatin jihar, Muhammad Bello Sifawa, ya yaba wa DSS bisa bajintar da suka yi na ceto mutanen.

Ya kuma tabbatar wa da hukumomin tsaro a jihar cewa gwamnatin jihar na ci gaba da bayar da goyon baya don tabbatar da tsaro a jihar.

“Mun yaba wa DSS kan wannan aiki kuma a matsayinmu na gwamnati mai kishin kasa, za mu ci gaba da tallafa wa ma’aikata da sauran jami’an tsaro domin su gudanar da ayyukansu,” in ji Sifawa.

Sakataren ya kuma sanar da tallafin Naira 100,000 da gwamnatin jihar ta bai wa kowane daga cikin wadanda aka ceto daga hannun ‘yan bindigar.

MASU ALAKA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
Next Post
Kwamishinan ‘Yansandan Zamfara Ya Bayar Da Cek Na Sama Da Miliyan 50 Ga Iyalan ‘Yansandan Da Suka Rasu

Kwamishinan ‘Yansandan Zamfara Ya Bayar Da Cek Na Sama Da Miliyan 50 Ga Iyalan ‘Yansandan Da Suka Rasu

LABARAI MASU NASABA

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
DSS

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
DSS

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.