ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Ceto Mutane 7 Da Aka Sace A Sakkwato 

by Sadiq
2 years ago
DSS

Rundunar ‘yansandan farin kaya (DSS) a Jihar Sakkwato, ta mika wasu mutane bakwai da ta ceto ga gwamnatin jihar, kasa da sa’o’i 24 da sace su.

Da yake bayyana yadda aka kubutar da wadanda lamarin ya shafa, daraktan DSS a jihar, Abdulfatah Olawuno, ya ce sun samu labarin sace mutanen da ‘yan bindiga suka yi a kauyen Gundungul.

  • Shugaban Kasar Suriname: Tunanin Shugaba Xi Jinping Ya Samar Da Sabuwar Hanyar Bunkasa Duniya
  • PDP Ta Lashi Takobin Warware Rikicin Shugabancinta A Watan Agusta

“A yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa kauyen Gundungul, jami’an DSS sun yi artabu da ‘yan bindigar.

ADVERTISEMENT

“Tun da farko ‘yan bindigar sun kashe mutane biyu a kauyen Gundungul kafin su yi awon gaba da mutanen da aka ceto.

“Dukkanin mutanen bakwai da aka ceto DSS ta gwada lafiyarsu, kafin mika su ga gwamnatin jihar,” in ji Olawuno.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Ya kara tabbatar da shirin hukumar na tabbatar da tsaro tare da neman goyon bayan al’ummar Jihar Sakkwato.

Da yake karbar wadanda aka ceto a madadin gwamnatin jihar, sakataren gwamnatin jihar, Muhammad Bello Sifawa, ya yaba wa DSS bisa bajintar da suka yi na ceto mutanen.

Ya kuma tabbatar wa da hukumomin tsaro a jihar cewa gwamnatin jihar na ci gaba da bayar da goyon baya don tabbatar da tsaro a jihar.

“Mun yaba wa DSS kan wannan aiki kuma a matsayinmu na gwamnati mai kishin kasa, za mu ci gaba da tallafa wa ma’aikata da sauran jami’an tsaro domin su gudanar da ayyukansu,” in ji Sifawa.

Sakataren ya kuma sanar da tallafin Naira 100,000 da gwamnatin jihar ta bai wa kowane daga cikin wadanda aka ceto daga hannun ‘yan bindigar.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Kwamishinan ‘Yansandan Zamfara Ya Bayar Da Cek Na Sama Da Miliyan 50 Ga Iyalan ‘Yansandan Da Suka Rasu

Kwamishinan ‘Yansandan Zamfara Ya Bayar Da Cek Na Sama Da Miliyan 50 Ga Iyalan ‘Yansandan Da Suka Rasu

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.