• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Nemi Saki A Kotu Saboda Mijinta Ya Yi Hadarin Mota   

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rashin zaman da alkalin kotun Shari’a Musulunci ta daya ta Magajin Gari da ke a Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa, domin ci gaba da sauraron karar da wata mata mai suna Khadijah Aliyu Nalado ta shigar da mijinta mai suna Malam Jamilu, a kan takaddamar saki ya janyo tsaiko ga shari’ar da ake yi mai dauke da lambar kara ta 4861023. 

A zaman da Kotun ta yi a watan Fabirairun 2024, mai karar Khadijah, ta shigar da karar mijinta Jamilu ne, inda ta bukaci kotun ta raba aurenta na shekara uku da suka yi.

  • Tinubu Zai Kaddamar Da Motoci 2,700 Masu Amfan Da Iskar Gas A Watan Mayu
  • PDP Ta Lashi Takobin Warware Rikicin Shugabancinta A Watan Agusta

A wannan zaman na Fabirairun 2024, Jamilu ya shaida wa kotun cewa, kawai zai amince da bukatar Khadija ne idan ta biya shi Naira miliyan bakwai a matsayin ‘ Khul’i’.

Haka zalika, ya shaida wa kotun cewa, a cikin sama da shekaru biyu ya kashe Naira miliyan 2.5 a kan karatunta na Boko, tare da kuma akwatunan da ya saya mata shake da tufafi, inda kudin da ya kashe a kansu suka kai Naira miliyan 2.5, kari da wasu kudaden da ya kashe na al’adar yin aure.

Bugu da kari, ya kuma shaida wa kotun cewa, Khadijah wadda ya auro ta a Kofar Kibo a Garin Zariya, don Allah ya jarrabe shi da yin wani mummunar hatsari da motarsa, sai ta guje shi, bisa tunaninta cewa, ba zai warke daga raunukan da ya samu a lolacin hatsarin ba.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Ya kara da cewa, ta kuma yi ikirarin cewa, za ta biya ni ko nawa na kashe don in sake ta.

Sai dai, Khadija ta bakin lauyan da ya tsaya mata, Awwal Imam ya shaida wa kotun cewa, abin da za ta biya kawai shi ne Naira 100,000 kacal a matsayin sadakin da Jamilu ya bayar na aure.

Bayan wancan dage zaman kotun Jamilu ya yanke hukuncin sakinta ba tare da sai ta biya Naira miliyan bakwai da ya bukata a baya ba.

Jim kadan bayan rashin zaman Kotun, a hirarsa da LEADERSHIP Hausa a harabar Kotun Jamilu ya ce, tun bayan saki dayan da ya yi wa Khadijah ya bukaci ta kwashe kayanta daga gidansa amma ta ki.

Shi ma lauyan da ke tsaya wa Khadijah Awwal Imam ya ce, rashin zaman da kotun ba ta yi ba ne ya janyo ba a ci gaba da sauraron karar ba, amma muna fatan kafin lokacin da kotun za ta yi wani zaman, za a yi masalaha a bayan fagen kotun kan wannan takardamar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiya Ta Shirya Taro Kan Bunkasa Kimiyyar Karatu Daga Nesa

Next Post

Nijeriya Ta Kammala Bayar Da Horo Kan Fasahar Hada Magunguna

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

10 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

11 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

13 hours ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

1 week ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

1 week ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

1 week ago
Next Post
Nijeriya Ta Kammala Bayar Da Horo Kan Fasahar Hada Magunguna

Nijeriya Ta Kammala Bayar Da Horo Kan Fasahar Hada Magunguna

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.