ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Nemi Saki A Kotu Saboda Mijinta Ya Yi Hadarin Mota   

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Kotu

Rashin zaman da alkalin kotun Shari’a Musulunci ta daya ta Magajin Gari da ke a Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa, domin ci gaba da sauraron karar da wata mata mai suna Khadijah Aliyu Nalado ta shigar da mijinta mai suna Malam Jamilu, a kan takaddamar saki ya janyo tsaiko ga shari’ar da ake yi mai dauke da lambar kara ta 4861023. 

A zaman da Kotun ta yi a watan Fabirairun 2024, mai karar Khadijah, ta shigar da karar mijinta Jamilu ne, inda ta bukaci kotun ta raba aurenta na shekara uku da suka yi.

  • Tinubu Zai Kaddamar Da Motoci 2,700 Masu Amfan Da Iskar Gas A Watan Mayu
  • PDP Ta Lashi Takobin Warware Rikicin Shugabancinta A Watan Agusta

A wannan zaman na Fabirairun 2024, Jamilu ya shaida wa kotun cewa, kawai zai amince da bukatar Khadija ne idan ta biya shi Naira miliyan bakwai a matsayin ‘ Khul’i’.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, ya shaida wa kotun cewa, a cikin sama da shekaru biyu ya kashe Naira miliyan 2.5 a kan karatunta na Boko, tare da kuma akwatunan da ya saya mata shake da tufafi, inda kudin da ya kashe a kansu suka kai Naira miliyan 2.5, kari da wasu kudaden da ya kashe na al’adar yin aure.

Bugu da kari, ya kuma shaida wa kotun cewa, Khadijah wadda ya auro ta a Kofar Kibo a Garin Zariya, don Allah ya jarrabe shi da yin wani mummunar hatsari da motarsa, sai ta guje shi, bisa tunaninta cewa, ba zai warke daga raunukan da ya samu a lolacin hatsarin ba.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Ya kara da cewa, ta kuma yi ikirarin cewa, za ta biya ni ko nawa na kashe don in sake ta.

Sai dai, Khadija ta bakin lauyan da ya tsaya mata, Awwal Imam ya shaida wa kotun cewa, abin da za ta biya kawai shi ne Naira 100,000 kacal a matsayin sadakin da Jamilu ya bayar na aure.

Bayan wancan dage zaman kotun Jamilu ya yanke hukuncin sakinta ba tare da sai ta biya Naira miliyan bakwai da ya bukata a baya ba.

Jim kadan bayan rashin zaman Kotun, a hirarsa da LEADERSHIP Hausa a harabar Kotun Jamilu ya ce, tun bayan saki dayan da ya yi wa Khadijah ya bukaci ta kwashe kayanta daga gidansa amma ta ki.

Shi ma lauyan da ke tsaya wa Khadijah Awwal Imam ya ce, rashin zaman da kotun ba ta yi ba ne ya janyo ba a ci gaba da sauraron karar ba, amma muna fatan kafin lokacin da kotun za ta yi wani zaman, za a yi masalaha a bayan fagen kotun kan wannan takardamar.

Kotu
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Kammala Bayar Da Horo Kan Fasahar Hada Magunguna

Nijeriya Ta Kammala Bayar Da Horo Kan Fasahar Hada Magunguna

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.