ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Nemi Saki A Kotu Saboda Mijinta Ya Yi Hadarin Mota   

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Kotu

Rashin zaman da alkalin kotun Shari’a Musulunci ta daya ta Magajin Gari da ke a Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa, domin ci gaba da sauraron karar da wata mata mai suna Khadijah Aliyu Nalado ta shigar da mijinta mai suna Malam Jamilu, a kan takaddamar saki ya janyo tsaiko ga shari’ar da ake yi mai dauke da lambar kara ta 4861023. 

A zaman da Kotun ta yi a watan Fabirairun 2024, mai karar Khadijah, ta shigar da karar mijinta Jamilu ne, inda ta bukaci kotun ta raba aurenta na shekara uku da suka yi.

  • Tinubu Zai Kaddamar Da Motoci 2,700 Masu Amfan Da Iskar Gas A Watan Mayu
  • PDP Ta Lashi Takobin Warware Rikicin Shugabancinta A Watan Agusta

A wannan zaman na Fabirairun 2024, Jamilu ya shaida wa kotun cewa, kawai zai amince da bukatar Khadija ne idan ta biya shi Naira miliyan bakwai a matsayin ‘ Khul’i’.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, ya shaida wa kotun cewa, a cikin sama da shekaru biyu ya kashe Naira miliyan 2.5 a kan karatunta na Boko, tare da kuma akwatunan da ya saya mata shake da tufafi, inda kudin da ya kashe a kansu suka kai Naira miliyan 2.5, kari da wasu kudaden da ya kashe na al’adar yin aure.

Bugu da kari, ya kuma shaida wa kotun cewa, Khadijah wadda ya auro ta a Kofar Kibo a Garin Zariya, don Allah ya jarrabe shi da yin wani mummunar hatsari da motarsa, sai ta guje shi, bisa tunaninta cewa, ba zai warke daga raunukan da ya samu a lolacin hatsarin ba.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Ya kara da cewa, ta kuma yi ikirarin cewa, za ta biya ni ko nawa na kashe don in sake ta.

Sai dai, Khadija ta bakin lauyan da ya tsaya mata, Awwal Imam ya shaida wa kotun cewa, abin da za ta biya kawai shi ne Naira 100,000 kacal a matsayin sadakin da Jamilu ya bayar na aure.

Bayan wancan dage zaman kotun Jamilu ya yanke hukuncin sakinta ba tare da sai ta biya Naira miliyan bakwai da ya bukata a baya ba.

Jim kadan bayan rashin zaman Kotun, a hirarsa da LEADERSHIP Hausa a harabar Kotun Jamilu ya ce, tun bayan saki dayan da ya yi wa Khadijah ya bukaci ta kwashe kayanta daga gidansa amma ta ki.

Shi ma lauyan da ke tsaya wa Khadijah Awwal Imam ya ce, rashin zaman da kotun ba ta yi ba ne ya janyo ba a ci gaba da sauraron karar ba, amma muna fatan kafin lokacin da kotun za ta yi wani zaman, za a yi masalaha a bayan fagen kotun kan wannan takardamar.

Kotu
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Kammala Bayar Da Horo Kan Fasahar Hada Magunguna

Nijeriya Ta Kammala Bayar Da Horo Kan Fasahar Hada Magunguna

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.