ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Nemi Saki A Kotu Saboda Mijinta Ya Yi Hadarin Mota   

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Kotu

Rashin zaman da alkalin kotun Shari’a Musulunci ta daya ta Magajin Gari da ke a Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa, domin ci gaba da sauraron karar da wata mata mai suna Khadijah Aliyu Nalado ta shigar da mijinta mai suna Malam Jamilu, a kan takaddamar saki ya janyo tsaiko ga shari’ar da ake yi mai dauke da lambar kara ta 4861023. 

A zaman da Kotun ta yi a watan Fabirairun 2024, mai karar Khadijah, ta shigar da karar mijinta Jamilu ne, inda ta bukaci kotun ta raba aurenta na shekara uku da suka yi.

  • Tinubu Zai Kaddamar Da Motoci 2,700 Masu Amfan Da Iskar Gas A Watan Mayu
  • PDP Ta Lashi Takobin Warware Rikicin Shugabancinta A Watan Agusta

A wannan zaman na Fabirairun 2024, Jamilu ya shaida wa kotun cewa, kawai zai amince da bukatar Khadija ne idan ta biya shi Naira miliyan bakwai a matsayin ‘ Khul’i’.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, ya shaida wa kotun cewa, a cikin sama da shekaru biyu ya kashe Naira miliyan 2.5 a kan karatunta na Boko, tare da kuma akwatunan da ya saya mata shake da tufafi, inda kudin da ya kashe a kansu suka kai Naira miliyan 2.5, kari da wasu kudaden da ya kashe na al’adar yin aure.

Bugu da kari, ya kuma shaida wa kotun cewa, Khadijah wadda ya auro ta a Kofar Kibo a Garin Zariya, don Allah ya jarrabe shi da yin wani mummunar hatsari da motarsa, sai ta guje shi, bisa tunaninta cewa, ba zai warke daga raunukan da ya samu a lolacin hatsarin ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Ya kara da cewa, ta kuma yi ikirarin cewa, za ta biya ni ko nawa na kashe don in sake ta.

Sai dai, Khadija ta bakin lauyan da ya tsaya mata, Awwal Imam ya shaida wa kotun cewa, abin da za ta biya kawai shi ne Naira 100,000 kacal a matsayin sadakin da Jamilu ya bayar na aure.

Bayan wancan dage zaman kotun Jamilu ya yanke hukuncin sakinta ba tare da sai ta biya Naira miliyan bakwai da ya bukata a baya ba.

Jim kadan bayan rashin zaman Kotun, a hirarsa da LEADERSHIP Hausa a harabar Kotun Jamilu ya ce, tun bayan saki dayan da ya yi wa Khadijah ya bukaci ta kwashe kayanta daga gidansa amma ta ki.

Shi ma lauyan da ke tsaya wa Khadijah Awwal Imam ya ce, rashin zaman da kotun ba ta yi ba ne ya janyo ba a ci gaba da sauraron karar ba, amma muna fatan kafin lokacin da kotun za ta yi wani zaman, za a yi masalaha a bayan fagen kotun kan wannan takardamar.

Kotu
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Kammala Bayar Da Horo Kan Fasahar Hada Magunguna

Nijeriya Ta Kammala Bayar Da Horo Kan Fasahar Hada Magunguna

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.