ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za A Raba Ci Gaban Kasar Sin Da Gudunmuwar Mata Ba

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Hadaddiyar kungiyar mata ta kasar Sin, da hukumar hadin gwiwar neman ci gaban kasa da kasa ta kasar, sun kaddamar da wani sansanin ba da horo a fannin mu’amala, da hadin gwiwa ta fuskar samar da ci gaban harkokin mata na kasa da kasa. 

Hausawa kan ce ilmantar da mace guda, tamkar ilmantar da al’umma ne. Kamar yadda takwarorinsu maza suke taka rawa a harkokin da suka shafi shugabanci da tsara manufofi, su ma mata idan suka samu dama, za su iya bayar da kwatankwacin gudunmawar.

  • ‘Yan Kasuwar Afrika Sun Gano Zarafi Mai Kyau A Canton Fair
  • Shugaban Serbia: Zan Rubuta Wani Littafi Don Tunawa Da Hulda Ta Da Xi Jinping

Baya ga tallafawa a bangarori kamar na bunkasa tattalin arziki da ababen more rayuwa da sauransu, kasar Sin tana kuma mayar da hankali kan kowanne bangare da zai taimaka ga samar da ci gaba na bai daya, shi ya sa a ko da yaushe na kan bayyana ta a matsayin mai hangen nesa da kaifin basira. A zamana a kasar, na ga yadda ake bayar da muhimmanci ga harkokin mata da yadda ake ba su damarmaki daidai da takwarorinsu ba tare da nuna musu wariya ba. Kuma na ga yadda hakan ya ba mata damar taka rawa a fannoni daban-daban kama daga kimiyya da fasaha da tattalin arzikin da harkokin shugabanci da sauransu, har ma da yadda suka bayar da gudunmawa wajen fatattakar talauci, shi ya sa ba za a taba raba ci gaban da kasar Sin ta samu da gudunmawar mata ba.

ADVERTISEMENT

Ina da yakinin cewa, rawar da mata a kasar Sin ke takawa sakamakon damarmakin da aka ba su ne ya sa kasar ke wa kasashe masu tasowa sha’awar irin hakan. Duk da cewa, an bar mata a baya cikin al’amuran da suka shafi tafiyar da harkokin kasashe da ma duniya, lokaci bai kure ba na damawa da su.

Ba shakka, wannan yunkuri na kungiyar mata ta kasar Sin da hukumar neman ci gaban kasa da kasa ta kasar, ya bullo da kyakkyawar dabarar da za ta ba mata kwarin gwiwa, musamman na kasashenmu masu tasowa, ta yadda za su shiga a dama da su cikin muhimman harkokin kasa tare da bayar da irin nasu gudummawa ga ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kasashensu. (Faeza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Yan Sama Jannatin Shenzhou-17 Sun Dawo Doron Duniya

Yan Sama Jannatin Shenzhou-17 Sun Dawo Doron Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.