• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ci Tarar ‘Yansanda Naira Miliyan 300 Kan Kisan ‘Yan Shi’a A Zariya

byRabi'u Ali Indabawa
1 year ago
'yansanda

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Kaduna ta umurci hukumomin ‘yansanda da su biya zunzurutun kudi Naira miliyan 300 ga iyayen ‘yan Shi’a uku da ake zargin jami’anta sun kashe a lokacin da suke gudanar da muzahara a shekarar 2022 a Zariya.

Mai shari’a Hawa Buhari, a cikin hukuncin da ta yanke, ta ce “masu neman hakkokinsu kamar yadda doka ta yi umarnin a ba su a cikin sashe na 33, 38, 39, 40, 42 da 46 na kundin tsarin mulkin 1999 (da aka gyara); Umarni na 2, Dokoki na 1, 2, 3, 4, 11 da 12 na Dokokin Kare Hakki da nuna Mahimmanci (Tasirin Tilastawa) da tsarin Dokokin 2009; ya yi nuni da cewa; Ana aiwatar da doka ta 4, 8, 10, 11 da 12 na Yarjejeniya Ta Afirka ta 2004 game da ‘yancin dan’Adam da jama’a.”
Alkalin kotun ta ce adadin Naira miliyan 100 da ya zama dole a biya ga kowane iyayen mamacin, inda za a biya jimillar Naira miliyan 300, a matsayin diyya, sannan kuma gamayyar diyyar, za a rika samar da riba ta kashi 10 cikin 100 a duk shekara har sai an biya kudaden.

  • Wani Dansanda Mai Rakiyar Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja Ya Rasu Acikin Jirgin
  • Kotu Ta Hana ‘Yansanda Kama Shugabannin Jam’iyyar APC Da Suka Dakatar Da Ganduje A Kano

Mai shari’a Buhari, a hukuncin da ta yanke a ranar 22 ga Afrilu, 2024, tare da kwafin na hukuncin da aka bai wa manema labarai ranar Lahadi a Abuja, ya karfafa kararraki guda uku da makusantan mamatan uku suka shigar.

“Za a ba wa kowane iyayen mamaci Kudi Naira miliyan 100,000,000.00 a matsayin diyya da kuma jimillar diyyar za ta zama tare da ribar kashi 10 a duk shekara har sai an cika adadin.

“Wadanda aka yi kara za su nemi afuwar masu kara a bainar jama’a kowace rana saboda keta haddinsu da suka yi,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Za a iya tunawa cewa mutane uku ne da suka hada da; Magaji Yusuf, Muhammad Lawal da Aliyu Badamasi sun shigar da kara mai lamba: FHC/KH/KD/138/2022, FHC/KH/KD/140/2022 da FHC/KH/KD/146/2022 a gaban kotun.
Sun yi zargin cewa a ranar 8 ga Agusta, 2022, jami’an ‘yan sandan Nijeriya sun harbe Jafar Magaji, Aliyu Lawal da Muhsin Badamasi, a lokacin da suke gudanar da ibadarsu ta Muzaharar Ashura a Garin Zariya.

Sun kai karar Sufeto-Janar na ’yansanda (IGP), Mataimakin Sufeto-Janar na ’yansanda na shiyya ta 7, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Kaduna, AC Surajo Fana (Kwamandan yankin Zariya), Ibrahim Zubairu (Jami’in ’Yansanda, Kasuwar Mata, Sabon Garin). Zaria Dibision), da Kasim Muhammad (DPO, Zaria City Dibision) a matsayin wadanda ake kara na 1 zuwa na 6.

Masu neman a gabatar da karar a ranar 26 ga Satumba, 2022 da kuma gabatarwa a ranar 26 ga Satumba, 2022, ta tawagar lauyoyinsu da suka hada da H.G Magashi, M.D Abubakar da Dokta Yusha’u Shaikh, da sauran mutum bakwai.

Sun nemi a bayyana cewa harbin da aka yi wa Jafar Magaji, Aliyu Lawal da Muhsin Badamasi a ranar da ake gudanar da muzaharar a matsayin abin da ya saba wa doka, kuma ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa da kuma tauye hakkinsu na rayuwa kamar yadda sashe na 33 na kundin tsarin mulkin 1999 da sashe na 1999 ya tabbatar, da kuma Yarjejeniya 4 Ta Afirka Kan Hakkokin Dan’Adam da Jama’a Cap A9 LFN, 2004.

Don haka sun roki kotu da ta umarci wadanda ake kara tare da su biya su Naira miliyan 200 kowannensu saboda tauye hakkin ‘yan uwansu da suka rasu.

Haka kuma sun nemi oda, inda suka umurci wadanda ake kara da su rubuta takardar neman gafara ta hanyar bugawa a cikin jaridun kasar guda biyu da ke yawo a Arewacin Nijeriya.

Amma wadanda ake kara, a cikin kararsu ta farko mai kwanan wata da kuma gabatar da su a ranar 8 ga Nuwamba, 2022, sun nemi a ba da umarnin soke kararrakin ukun saboda rashin hukumci.

Bayan haka, sun kuma gabatar da takardar shaidar adawa da kara.

Sai dai mai shari’a Buhari ya amince da gabatar da lauyoyin wanda ya shigar da karar, kuma ya dauki hukumci kan lamarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version