• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani

by Leadership Hausa
1 year ago
in Adabi, Ilimi, Labarai
0
Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsofaffin daliban Sashen’ Koyar da Harsunan Nijeriya na Jami’ar Bayero ‘yan shekarar 2015 sun sabunta Dakin Karatu na Sashen tare da gyaran wasu sassa na Sashen a Jami’ar.

A ranar Alhamis 02 ga watan Mayun 2024 aka gudanar da kasaitaccen bikin bude Dakin Karatu na Marigayi Farfesa M.A.Z Sani da tsofaffin daliban Sashen suka sabunta shi bisa jagorancin shugaban daliban na 2015, Alhaji Hassan Baita Ubawaru, wanda ya samu wakilcin Sakataren Kungiyar daliban, Muhammad Bashir Amin.

Sakataren Kungiyar Dalibai 'Yan Ajin 2015, Muhammad Bashir Amin, yayin da yake yi wa Shugaban Jami'ar Bayero bayani yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani
Sakataren Kungiyar Dalibai ‘Yan Ajin 2015, Muhammad Bashir Amin, yayin da yake yi wa Shugaban Jami’ar Bayero bayani yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani
  • Za Mu Sabonta Dakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita
  • Jami’ar Bayero Kano Za Ta Karrama Sanata Barau Da Adesina Da Digirin Girmamawa

A nasa jawabin Shugaban Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya na Jami’ar Bayero, Dr. Jibril Shu’aibu Adamu, ya yaba da kokarin daliban ya kuma sanarwa da Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, irin kokarin da daliban suke yi na tallafawa Sashen, inda ya ce ko a kwanan nan tsofaffin daliban sun bai wa Sashen sababbin injinan nadar bayanan takardu uku tare da gyaran wasu sassa na Sashen.

Shugaban Jami'ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas da Dr. Jibril S. Adamu da Alh. Baita Ubawaru yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani
Shugaban Jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas da Dr. Jibril S. Adamu da Alh. Baita Ubawaru yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani

A nasa jawabin, Shugaban Jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya yaba da kokarin daliban da irin tallafin da suke bai wa Sashen, ya kuma yi alkawarin ci gaba da tallafawa Sashen daga bangaren shugabancin Jami’ar.

Sagir ya ce, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya shi ne Sashe daya rak da ya fi kowane Sashen hulda da kasashen waje da suka hada da kasar Sin da Holandiya da Jamus da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

A jawabin shugaban daliban, Alh. Hassan Baita Ubawaru, wanda ya samu wakilcin Sakataren kungiyar daliban, Muhammad Bashir Amin, ya ce, za su ci gaba da tallafawa Sashen ta bangarori da dama, tare da aiki kafada-kafada da juna don ganin an inganta harkokin koyo d koyarwa da bunkasa Harshe da Adabi da Al’adun Hausawa.

Alh. Baita Ubawaru yayin da yake jawabi a wurin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani a Jami'ar Bayero.
Alh. Baita Ubawaru yayin da yake jawabi a wurin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani a Jami’ar Bayero.

A nasa jawabin, Alh. Baita Ubawaru, wanda shi ne mahaifin shugaban daliban na 2015, kuma daya daga cikin wandanda suka tallafawa Shugaban Jami’ar wajen kaddamar da bude Dakin Karatun a yayin bikin, ya bayyana farin cikinsa tare da fatan Dakin Karatun ya zama mai amfanar da daliban Sashen da sauran al’umma baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUKDakin KaratuJami'ar Bayero
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fatima Mai Zogale: Baturiyar Da Allah Ya Yi A Dare Daya

Next Post

Shawara Ya Kamata Malamai Su Rika Bai Wa ‘Yan Kannywood Ba Zagi Ba – Daushe

Related

Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC
Labarai

Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

5 hours ago
Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato
Labarai

Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

6 hours ago
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

8 hours ago
Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

9 hours ago
An Fara Binciken Bidiyon Ciyar Da Sojoji Garaugarau
Labarai

An Fara Binciken Bidiyon Ciyar Da Sojoji Garaugarau

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

11 hours ago
Next Post
Shawara Ya Kamata Malamai Su Rika Bai Wa ‘Yan Kannywood Ba Zagi Ba – Daushe

Shawara Ya Kamata Malamai Su Rika Bai Wa ‘Yan Kannywood Ba Zagi Ba - Daushe

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

July 24, 2025
Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

July 24, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

July 24, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

July 24, 2025
Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

July 24, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

July 24, 2025
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

July 24, 2025
Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

July 24, 2025
Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

July 24, 2025
Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

July 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.