• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Musanta Iƙirarin Binance Na Zargin Cin Hancin Dala Miliyan 150

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Nijeriya Ta Musanta Iƙirarin Binance Na Zargin Cin Hancin Dala Miliyan 150
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta mayar da martani kan iƙirarin da Shugaban kamfanin Binance, Richard Teng, ya yi na cewa wai wasu jami’an gwamnatin Nijeriya sun buƙaci a ba su cin hanci da kuɗaɗen kirifto don warware binciken laifuffukan da ake yi wa masa.

Teng ya yi wannan iƙirarin ne a wani shafin yanar gizon da kafafen watsa labarai na ƙasashen waje suka buga ranar Talata, inda ya ƙara da cewa lauyan Binance ya ƙi amincewa da tayin.

  • CBN Ya Bayyana Sunayen Bankuna 41 Da Ya Aminta Da Ingancinsu A Nijeriya 

 

Da yake mayar da martani kan zargin a ranar Laraba, Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Teng ya ƙare da “dabarun karkatar da hankulan jama’a da kuma yunƙurin yin ɓatanci da kamfanin ke yi don kawar da tuhume-tuhume masu tsanani da yake fuskanta a Nijeriya.”

A wata sanarwar da Rabiu Ibrahim, mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai ya sanya wa hannu, ministan ya jaddada cewa wanda ya kafa Binance, Changpeng Zhao, ya aikata irin wannan laifin na halasta kuɗaɗen haram a Amurka, kuma a halin yanzu yana zaman gidan yari, lamarin da ke nuni da cewa ya kamata kamfanin na kirifto ya miƙa kan sa ga hukuma domin bincike.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

Ya ce: “Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta na sane da yunƙurin da Binance ke yi na wanke sunan sa a matsayin kamfanin da ba ya bin ƙa’ida da dokokin da ke jagorantar harkokin kasuwanci a ƙasashe masu cin gashin kai.

“A cikin wani saƙon da ya wallafa a shafin yanar gizon da yawancin kafafen watsa labarai na ƙasa da ƙasa suka wallafa a yanzu, Shugaban Binance Richard Teng, ya zargi kan wasu jami’an gwamnatin Nijeriya da ba a san ko su waye ba da cin hanci da rashawa, wanda ya yi iƙirarin cewa sun buƙaci a biya kuɗaɗen kirifto dala miliyan 150 don warware binciken laifuffukan da ake yi wa kamfanin.

“Wannan iƙirarin na Shugaban Binance ba gaskiya ba ne. Ba komai ba ne illa dabarar karkatar da hankulan jama’a da kuma yunƙurin yin ɓatanci da kamfanin ke yi don kawar da tuhume-tuhume masu tsanani da yake fuskanta a Nijeriya.

“Gaskiyar wannan al’amari ita ce ana binciken Binance a Nijeriya ne saboda yadda ya ba da damar yin amfani da dandalin sa wajen halasta kuɗaɗen haram, bayar da tallafi ga ta’addanci, da kuma tafka maguɗin kuɗaɗen ƙasashen waje ta hanyar cinikin haramun.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BinanceCin HanciJami'an GwamnatiKasashen WajeRashawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsaron Yanar Gizo: TUC Ta Yi Barazanar Shiga Zanga-zanga A Nijeriya

Next Post

An Gabatar Da Shirin Talabijin Mai Suna Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So A Hungary

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

6 hours ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

7 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

8 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

10 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

12 hours ago
Next Post
An Gabatar Da Shirin Talabijin Mai Suna Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So A Hungary

An Gabatar Da Shirin Talabijin Mai Suna Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So A Hungary

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.