• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Gombe, na shirin farfado da Masana’antun Auduga ta hanyar rugumar shirin gwamnatin tarayya na farfado da noman auduga, don bunkasa tattalin arzikin al’ummar jihar.

Gwamnan Jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya ne ya bayyana hakan, yayin da yake gana wa da tawagar ‘Kamfanin Arise Integrated Industrial Platform’ karkashin jagorancin Babban Mataimakin Shugaban Kamfanin Jacky Ribiere, a fadar gwamnatin jihar ta Gombe.

  • Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli
  • Hajj 2024: NAHCON Ta Bukaci ‘Yan Jarida Su Yi Riko Da Gaskiya

Yahaya, wanda ya yi tsokaci a kan kokarin gwamnatin tarayya na sake farfado da noman auduga da masakun tufafi a Nijeriya, ya ba da tabbacin bayar da gagarumin goyon baya, domin saukaka farfado da noman na auduga a fadin jihar ta Gombe tare da yaba wa da kuma jaddada hangen nesan Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a kan hakan.

Ya kara da cewa, kasancewar Gombe jiha ce mai samar da auduga da wasu takwarorinta na Arewa kamar Katsina, Kaduna, da kuma Zamfara, akwai fatan sake farfado da noman auduga tare da sarrafa Irinta kamar yadda shirin farfado da noman audugan na gwamnatin ya kuduri aniyar yi.

Gwamna Inuwa, ya sake jaddada muhimmancin hada hannu da masu ruwa da tsaki; wadanda suka hada da Kungiyar Manoman Auduga ta Kasa (NACOTAN), don samar da cikakken tsarin farfado da noma da kuma sarrafa audugar.

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Haka zalika, ya bayyana damammakin da ake da su na damawa da manoma a Karamar Hukumar Balanga da wasu sauran Kananan Hukumomin Kudancin Jihar, wadanda suke da matukar muhimmanci wajen noman wannan auduga a jihar.

“Sake farfado da sana’ar noman auduga, zai magance rashin aikin yi a tsakanin matasan Nijeriya tare da farfado da tattalin arzikin wannan kasa,” in ji Gwamnan. Sannan, ya bayyana Jihar Gombe a matsayin daya daga cikin jihohin da ake noman audugar, ya kuma yi alkawarin ci gaba da ba da kwarin guiwa ga noman na auduga, domin samun riba mai yawan gaske.

Bugu da kari, ya kuma shaida wa bakin nasa cewa, ganin yadda aka kafa sansanin masana’antu na Muhammadu Buhari, mai fadin hekta 1,000 a kusa da tashar wutar lantarki ta Dadinkowa; mai karfin megawat 40 da kamfanonin gurzan auduga da ake da su a Jihar Gombe, hakan zai tallafa wajen sake farfado da bangaren noman na auduga.

Har ila yau, taron ya samu halartar Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, da Kwamishinan Ciniki, Masana’antu da Yawon Bude Ido, Nasiru Mohammed Aliyu da kuma takwaransa na Ma’aikatar Noma da Kiwo, Dakta Barnabas Malle; kamar yadda Ismaila Uba Misilli, Babban Daraktan Yada Labarun Gwamnan Jihar na Gombe ya nakalto.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombeNoman Auduga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karancin Abinci Na Kara Ta’azzara A Nijeriya

Next Post

Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

7 hours ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

1 week ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1 week ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Next Post
Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.