ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Auduga

Gwamnatin Jihar Gombe, na shirin farfado da Masana’antun Auduga ta hanyar rugumar shirin gwamnatin tarayya na farfado da noman auduga, don bunkasa tattalin arzikin al’ummar jihar.

Gwamnan Jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya ne ya bayyana hakan, yayin da yake gana wa da tawagar ‘Kamfanin Arise Integrated Industrial Platform’ karkashin jagorancin Babban Mataimakin Shugaban Kamfanin Jacky Ribiere, a fadar gwamnatin jihar ta Gombe.

  • Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli
  • Hajj 2024: NAHCON Ta Bukaci ‘Yan Jarida Su Yi Riko Da Gaskiya

Yahaya, wanda ya yi tsokaci a kan kokarin gwamnatin tarayya na sake farfado da noman auduga da masakun tufafi a Nijeriya, ya ba da tabbacin bayar da gagarumin goyon baya, domin saukaka farfado da noman na auduga a fadin jihar ta Gombe tare da yaba wa da kuma jaddada hangen nesan Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a kan hakan.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, kasancewar Gombe jiha ce mai samar da auduga da wasu takwarorinta na Arewa kamar Katsina, Kaduna, da kuma Zamfara, akwai fatan sake farfado da noman auduga tare da sarrafa Irinta kamar yadda shirin farfado da noman audugan na gwamnatin ya kuduri aniyar yi.

Gwamna Inuwa, ya sake jaddada muhimmancin hada hannu da masu ruwa da tsaki; wadanda suka hada da Kungiyar Manoman Auduga ta Kasa (NACOTAN), don samar da cikakken tsarin farfado da noma da kuma sarrafa audugar.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Haka zalika, ya bayyana damammakin da ake da su na damawa da manoma a Karamar Hukumar Balanga da wasu sauran Kananan Hukumomin Kudancin Jihar, wadanda suke da matukar muhimmanci wajen noman wannan auduga a jihar.

“Sake farfado da sana’ar noman auduga, zai magance rashin aikin yi a tsakanin matasan Nijeriya tare da farfado da tattalin arzikin wannan kasa,” in ji Gwamnan. Sannan, ya bayyana Jihar Gombe a matsayin daya daga cikin jihohin da ake noman audugar, ya kuma yi alkawarin ci gaba da ba da kwarin guiwa ga noman na auduga, domin samun riba mai yawan gaske.

Bugu da kari, ya kuma shaida wa bakin nasa cewa, ganin yadda aka kafa sansanin masana’antu na Muhammadu Buhari, mai fadin hekta 1,000 a kusa da tashar wutar lantarki ta Dadinkowa; mai karfin megawat 40 da kamfanonin gurzan auduga da ake da su a Jihar Gombe, hakan zai tallafa wajen sake farfado da bangaren noman na auduga.

Har ila yau, taron ya samu halartar Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, da Kwamishinan Ciniki, Masana’antu da Yawon Bude Ido, Nasiru Mohammed Aliyu da kuma takwaransa na Ma’aikatar Noma da Kiwo, Dakta Barnabas Malle; kamar yadda Ismaila Uba Misilli, Babban Daraktan Yada Labarun Gwamnan Jihar na Gombe ya nakalto.

Auduga
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.