• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Cinnawa Masallaci Wuta, Mutane 11 Sun Rasu A Kano

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Al'ajabi, Manyan Labarai
0
Bayan Cinnawa Masallaci Wuta, Mutane 11 Sun Rasu A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu an tabbatar da mutuwar mutane 11 bayan da wani matashi mai suna Shafi’u Abubakar ya yi kwantan ɓauna ya cinnawa wasu masallata wuta lokacin da suke tsaka da yin sallar Asuba a garin Gadan da ke ƙaramar hukumar Gazawa.

Kawo yanzu an tabbatar da mutuwar mutane 11 bayan da wani matashi mai suna Shafi’u Abubakar ya yi kwantan ɓauna ya cinnawa wasu masallata wuta lokacin da suke tsaka da yin sallar Asuba a garin Gadan da ke ƙaramar hukumar Gazawa

  • An Dakatar Da Likita Saboda Sakaci A Jihar Kano
  • Matashi Ya Banka Wa Masallaci Wuta Yayin Da Ake Sallah A Kano

Iftila’in dai ya faru ne a jiya Laraba, in da Matashin mai shekaru 38, ya ce ya yi hakan ne sakamakon fushin rikicin rabon gado, bayan ya cimma wutar ne ya kuma kulle ƙofar masallacin don kar wani ya samu damar ficewa.

An dai ruwaito cewa lokacin da lamarin ya afku akwai kimanin mutane 40 da suke sallar Asuba a cikin masallacin, bayan samun damar fitar da su ne aka garzaya asibiti domin duba lafiyarsu, sai dai kash 11 daga cikinsu sun riga mu tafiya gidan gaskiya.

Wani mazaunin garin mai suna Rabi’u Gadan ya shaidawa LEADERSHIP Hausa cewa; tuni dai har an gudanar da jana’izar 8 daga cikinsu Kuma na shirye-shiryen yinta ragowar ukun. Rabi’u ya ce harin masallacin ba wannan ne ta’addacin da matashi Shafi’u ya taɓa yi ba a ƙauyen nasu, domin ya taɓa yi wa yayanninsa biyu rutse kuma ya kai kansa wurin ƴan sanda ya ce wai ya kashe su.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Wani mazaunin garin mai suna Malam Garba ya ce; Da ma can matashin fitinanne ne don har an taɓa kai shi gidan asibitin masu motsin ƙwaƙwalwa amma likita suka ce lafiyarsa ƙalau, kuma a lokacin da ya ƙalubalanci danginsa da cewa lallai sai sun ba shi rabon gadonsa, sai ku raba suka ba shi. Don haka lafiyarsa kalau ya cinna wutar, kuma biyu daga cikin waɗanda suka rasu kawunnansa ne.

Shi dai wannan matashi yanzu haka yana can tsare a hannun jami’an tsaro ana cigaba da bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yansandan jihar KanoAsibitiDSSkano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’ar FUBK Ta Gudanar Da Bikin Ɗaukar Sabbin Ɗalibai 2, 217 A Kebbi

Next Post

Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

2 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

14 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

19 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

23 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Next Post
Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe

Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.