ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gwamna Inuwa

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da zaƙulo damammakin da ke tattare da harkar noma a Jihar Gombe ta hanyar tallafawa masana’antun da suka jiɓinci harkar noma, waɗanda ya ce su na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban tattalin arziƙi da zamantakewa.

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin da ya ƙaddamar da kamfanin sarrafa taki da sinadaran noma na Al-Yuma a garin Kwadon da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba.

  • Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa
  • Karin Kudin Hajji: Gwamna Inuwa Ya Tallafa Wa Maniyyatan Gombe Da Naira 500,000 Kowanne

Ya bayyana irin rawar da kamfanin zai taka wajen samar da ayyukan yi da kayan noma don bunƙasa samar da abinci da wadatarsa.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana ƙudurinsa na ci gaba da bunƙasa harkar noma a bisa ƙudurin sabunta fata na Shugaba Tinubu, musamman ƙudurinsa na bunƙasa noma don tabbatar da isasshen abinci a ƙasar nan.

“Kuma tun hawanmu kan karagar mulki a 2019, muke mayar da hankali kan samar da abinci. Domin mun yi imanin cewa ci gabanmu ya ta’allaka ne da noma,” in ji Gwamna Inuwa.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Gwamna Inuwa
Wani yanki daga cikin masana’antar

Gwamnan ya ci gaba da cewa, akwai wadatacciyar ƙasa mai faɗin gaske a Gombe, ga kuma yawan al’ummar da sun kai su samar da wadataccen abinci, yana mai jaddada cewa, “Babu dalilin da zai sa Nijeriya ta dogara da shigo da abinci daga ƙasashen waje alhali muna da abin da za mu iya ciyar da kanmu”.

Da ya ke yabawa da irin rawar da ‘yan kasuwa ke takawa wajen rage zaman banza, Gwamna Inuwa ya ce “Duk da cewa samar da ayyukan yi shi ne abu na farko da ya rataya a wuyan ‘yan kasuwa, aikin gwamnati shi ne ta samar da kyakkyawan yanayin haɓaka kasuwancin, don haka a shirye muke mu tallafawa duk wani dan kasuwa da ke son ya kafa kasuwancinsa a Jihar Gombe”.

Ya ce irin nasarorin da Gombe ta samu har sau biyu a fagen sauƙaƙa kasuwanci da kuma samun kyakkyawan matsayi har uku a fannin kyautata tattalin arziki da zamantakewa a matsayin shaida kan ƙudurin gwamnatinsa na samar da yanayi mai aminci don ‘yan kasuwa su ci gaba.

Gwamna Inuwa

Gwamnan ya sanar da kawo karshen rabon tallafin abinci, maimakon hakan ya ce taki za a samar don ƙarfafa gwiwar jama’a su koma gona don magance matsalolin tattalin arziƙi.

Gwamna Inuwa ya sanar da sayan taki tan dubu 200 daga sabon kamfanin na Alyuma don rabawa manoman Jihar Gombe. “Za mu sayi taki don tallafa muku idan kun shirya komawa noma,” in ji shi.

Tun da farko a jawabinsa na maraba, Shugaban Kamfanin taki da sinadaran na Al-Yuma, Alhaji Yusuf Ali Yusuf, wanda ya samu wakilcin Manajan Daraktan Kamfanin, Dakta Faruk Hamza, ya ce kyakkyawan yanayin kasuwanci da gwamnan ya samar a Jihar Gombe ne ya ƙarfafa musu kafa kamfanin a jihar.

Ya ce Gwamna Inuwa Yahaya ya samar da ingantattun manufofi tare da goyon baya daga gwamnatinsa ga ‘yan kasuwa.

Ya kuma yabawa Gwamna Inuwa bisa kishinsa ga noma, yana mai cewa kyawawan manufofinsa ne suka zaburar da su. “Kokarinka ya taimaka matuƙa wajen kawo wannan kamfani Jihar Gombe, kuma ga shi a ƙarshe aikin ya yi nasara,” in ji shi.

Ya ce kamfanin na da ƙarfin samar da tan dubu 120 na takin zamani kala-kala a duk shekara, “Har ila yau, muna samar da takin da zai dace da kowace irin ƙasa ko amfanin gona,” in ji shi.

Gwamna Inuwa

A nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Yamaltu Alhaji Abubakar Aliyu, ya godewa Gwamna Inuwa bisa samar da yanayi na zaman lafiya da kwanciyar hankali don kafa irin waɗannan kamfanoni.

Gwamna Inuwa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Hisbah Ta Haramtawa Maza Masu Kiɗan DJ Shiga Wurin Shagalin Bikin Mata A Jihar Kano

Hisbah Ta Haramtawa Maza Masu Kiɗan DJ Shiga Wurin Shagalin Bikin Mata A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.