ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbatar Da Cikakken ’Yancin Kai, Ita Ce Za Ta Kyautata Dangantakar Sin Da Japan Da Korea Ta Kudu

by CGTN Hausa
1 year ago
Japan

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Bayan dakatarwa ta sama da shekaru 4, a farkon wannan mako an gudanar da taron shugabannin kasashen Sin da Japan da Korea ta Kudu. Kuma yayin jawabin da ya gabatar ga taron harkokin kasuwanci karo na 8 tsakanin kasashen uku, firaministan Sin Li Qiang ya bukaci kasashen su dakile duk wani kutse daga waje da zai illata dangantakarsu.
Hakika, lokacin da aka shafe ba tare da gudanar da taron kasashen 3 ba, ya nuna tsanani da kuma girman yadda wasu kasashe daga waje ke tsoma baki cikin harkokin wadannan makwabta, lamarin da za a iya cewa bai amfani yankin da komai ba sai tankiya. Kasancewar Sin da Japan da Korea ta kudu matsayin makwabta, abu ne mai muhimmanci dake tattare da dimbin damarmaki. Kasashen dake makwabtaka da juna da kamanceceniyar al’adu, na da damarmakin raya kansu cikin aminci da girmama juna, idan har suka toshe kutse daga waje. A ganina, ci gaban daya daga cikinsu, nasara ce ga dukkansu, domin abu ne da kowannensu zai iya cin gajiyarsa. Kana kyautatuwar dangantaka a tsakaninsu, ita ce za ta bunkasa musaya da fahimtar juna tsakanin jama’arsu, wanda zai kai ga samun al’ummomi masu jituwa dake zaune lafiya, kuma ’yan uwa juna.

Hadin gwiwa tsakanin bangarorin 3 shi ne zai ba su damar kara fahimtar juna da dinke duk wata baraka ko sabanin da za a iya samu a tsakaninsu. Bai kamata wasu daga cikinsu su rika barin wasu daga waje na tsoma baki cikin harkokinsu, ko jan ragamar harkokin da su ta shafa ba. Mai daki aka ce, shi ya san inda yake masa yoyo. Don haka, babu wata kasa daga waje da za ta fi su sanin yanayin da suke ciki da kuma bukatun da suke da shi, haka kuma babu wata daga waje da za ta fi su iya warware sabaninsu da kuma samar musu da hanyar raya kansu. Barin wata kasa tana hure musu kunne, tamkar tsaiko ne ga cikakken ’yancin da suke da shi a matsayinsu na kasashe.

  • Mozambique: An Shirya Maido Da Noman Alkama Bisa Tallafin Fasahohin Kasar Sin
  • Kotu Ta Hana Hukumomin Tsaro Tumɓuke Sarki Sanusi II

Ci gaban yankin da kwanciyar hankalinsa, ya dogara ne ga yunkurin kasashen Korea ta Kudu da Japan na kare cikakken ’yancin kansu, ta hanyar toshe duk wata kafa ta tsoma baki cikin harkokin yankin da kuma sanya muradun yankin a gaban komai. Kowa dai ya san kasar Sin kasa ce dake tabbatar da cikakken ikonta, kuma ba ’yar amshin shata ba ce, haka kuma ba ta tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe.

ADVERTISEMENT

Fatan ita ce, kasashen Korea ta Kudu da Japan za su gyara kuskurensu, su sanya muradun al’ummominsu da na makwabtansu gaba da komai, kana su yi hadin gwiwa bisa gaskiya da girmama juna domin tabbatar da ci gaban yankin da ma kwanciyar hankalinsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia
Daga Birnin Sin

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana
Daga Birnin Sin

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

'Yansanda Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kwato Kudin Fansa A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.