ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbatar Da Cikakken ’Yancin Kai, Ita Ce Za Ta Kyautata Dangantakar Sin Da Japan Da Korea Ta Kudu

by CGTN Hausa
2 years ago
Japan

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Bayan dakatarwa ta sama da shekaru 4, a farkon wannan mako an gudanar da taron shugabannin kasashen Sin da Japan da Korea ta Kudu. Kuma yayin jawabin da ya gabatar ga taron harkokin kasuwanci karo na 8 tsakanin kasashen uku, firaministan Sin Li Qiang ya bukaci kasashen su dakile duk wani kutse daga waje da zai illata dangantakarsu.
Hakika, lokacin da aka shafe ba tare da gudanar da taron kasashen 3 ba, ya nuna tsanani da kuma girman yadda wasu kasashe daga waje ke tsoma baki cikin harkokin wadannan makwabta, lamarin da za a iya cewa bai amfani yankin da komai ba sai tankiya. Kasancewar Sin da Japan da Korea ta kudu matsayin makwabta, abu ne mai muhimmanci dake tattare da dimbin damarmaki. Kasashen dake makwabtaka da juna da kamanceceniyar al’adu, na da damarmakin raya kansu cikin aminci da girmama juna, idan har suka toshe kutse daga waje. A ganina, ci gaban daya daga cikinsu, nasara ce ga dukkansu, domin abu ne da kowannensu zai iya cin gajiyarsa. Kana kyautatuwar dangantaka a tsakaninsu, ita ce za ta bunkasa musaya da fahimtar juna tsakanin jama’arsu, wanda zai kai ga samun al’ummomi masu jituwa dake zaune lafiya, kuma ’yan uwa juna.

Hadin gwiwa tsakanin bangarorin 3 shi ne zai ba su damar kara fahimtar juna da dinke duk wata baraka ko sabanin da za a iya samu a tsakaninsu. Bai kamata wasu daga cikinsu su rika barin wasu daga waje na tsoma baki cikin harkokinsu, ko jan ragamar harkokin da su ta shafa ba. Mai daki aka ce, shi ya san inda yake masa yoyo. Don haka, babu wata kasa daga waje da za ta fi su sanin yanayin da suke ciki da kuma bukatun da suke da shi, haka kuma babu wata daga waje da za ta fi su iya warware sabaninsu da kuma samar musu da hanyar raya kansu. Barin wata kasa tana hure musu kunne, tamkar tsaiko ne ga cikakken ’yancin da suke da shi a matsayinsu na kasashe.

  • Mozambique: An Shirya Maido Da Noman Alkama Bisa Tallafin Fasahohin Kasar Sin
  • Kotu Ta Hana Hukumomin Tsaro Tumɓuke Sarki Sanusi II

Ci gaban yankin da kwanciyar hankalinsa, ya dogara ne ga yunkurin kasashen Korea ta Kudu da Japan na kare cikakken ’yancin kansu, ta hanyar toshe duk wata kafa ta tsoma baki cikin harkokin yankin da kuma sanya muradun yankin a gaban komai. Kowa dai ya san kasar Sin kasa ce dake tabbatar da cikakken ikonta, kuma ba ’yar amshin shata ba ce, haka kuma ba ta tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe.

ADVERTISEMENT

Fatan ita ce, kasashen Korea ta Kudu da Japan za su gyara kuskurensu, su sanya muradun al’ummominsu da na makwabtansu gaba da komai, kana su yi hadin gwiwa bisa gaskiya da girmama juna domin tabbatar da ci gaban yankin da ma kwanciyar hankalinsa.

Japan
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

'Yansanda Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kwato Kudin Fansa A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.