• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbatar Da Cikakken ’Yancin Kai, Ita Ce Za Ta Kyautata Dangantakar Sin Da Japan Da Korea Ta Kudu

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Tabbatar Da Cikakken ’Yancin Kai, Ita Ce Za Ta Kyautata Dangantakar Sin Da Japan Da Korea Ta Kudu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan dakatarwa ta sama da shekaru 4, a farkon wannan mako an gudanar da taron shugabannin kasashen Sin da Japan da Korea ta Kudu. Kuma yayin jawabin da ya gabatar ga taron harkokin kasuwanci karo na 8 tsakanin kasashen uku, firaministan Sin Li Qiang ya bukaci kasashen su dakile duk wani kutse daga waje da zai illata dangantakarsu.

Hakika, lokacin da aka shafe ba tare da gudanar da taron kasashen 3 ba, ya nuna tsanani da kuma girman yadda wasu kasashe daga waje ke tsoma baki cikin harkokin wadannan makwabta, lamarin da za a iya cewa bai amfani yankin da komai ba sai tankiya. Kasancewar Sin da Japan da Korea ta kudu matsayin makwabta, abu ne mai muhimmanci dake tattare da dimbin damarmaki. Kasashen dake makwabtaka da juna da kamanceceniyar al’adu, na da damarmakin raya kansu cikin aminci da girmama juna, idan har suka toshe kutse daga waje. A ganina, ci gaban daya daga cikinsu, nasara ce ga dukkansu, domin abu ne da kowannensu zai iya cin gajiyarsa. Kana kyautatuwar dangantaka a tsakaninsu, ita ce za ta bunkasa musaya da fahimtar juna tsakanin jama’arsu, wanda zai kai ga samun al’ummomi masu jituwa dake zaune lafiya, kuma ’yan uwa juna.

  • Tsawon Hanyoyin Mota Da Sin Ta Shimfida A Kauyuka Ya Karu Da Kashi 18.5% A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2 Daga Daliban Da Suka Sace A Kogi

Hadin gwiwa tsakanin bangarorin 3 shi ne zai ba su damar kara fahimtar juna da dinke duk wata baraka ko sabanin da za a iya samu a tsakaninsu. Bai kamata wasu daga cikinsu su rika barin wasu daga waje na tsoma baki cikin harkokinsu, ko jan ragamar harkokin da su ta shafa ba. Mai daki aka ce, shi ya san inda yake masa yoyo. Don haka, babu wata kasa daga waje da za ta fi su sanin yanayin da suke ciki da kuma bukatun da suke da shi, haka kuma babu wata daga waje da za ta fi su iya warware sabaninsu da kuma samar musu da hanyar raya kansu. Barin wata kasa tana hure musu kunne, tamkar tsaiko ne ga cikakken ’yancin da suke da shi a matsayinsu na kasashe.

Ci gaban yankin da kwanciyar hankalinsa, ya dogara ne ga yunkurin kasashen Korea ta Kudu da Japan na kare cikakken ’yancin kansu, ta hanyar toshe duk wata kafa ta tsoma baki cikin harkokin yankin da kuma sanya muradun yankin a gaban komai. Kowa dai ya san kasar Sin kasa ce dake tabbatar da cikakken ikonta, kuma ba ’yar amshin shata ba ce, haka kuma ba ta tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe.

Fatan ita ce, kasashen Korea ta Kudu da Japan za su gyara kuskurensu, su sanya muradun al’ummominsu da na makwabtansu gaba da komai, kana su yi hadin gwiwa bisa gaskiya da girmama juna domin tabbatar da ci gaban yankin da ma kwanciyar hankalinsa.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

A shekarar 1999, shugabannin kasashen Sin, da Japan da Koriya ta Kudu sun fara yunkurin hadin gwiwa tsakanin kasashen uku, a yayin da suka halarci taron shugabannin kungiyar tarayyar kasashen kudu maso gabashin Asiya ta ASEAN, da na kasashen Sin, da Japan da Koriya ta Kudu. Ya zuwa yanzu, shekaru 25 ke nan, kuma cikin wadannan shekarun da suka gabata, hadin gwiwa tsakanin kasashen uku ta bunkasa cikin yanayin sauye-sauye, ta kuma ba da muhimmiyar gudummawa ga bunkasuwar tattalin arzikin yankin, da ma kasashen duniya baki daya, ta kuma ba da jagoranci ga dunkulewar yankin baki daya.

Manazarta na ganin cewa, a halin yanzu, ana fuskantar yanayin sauye-sauye a kasashen duniya, an kuma kasa samun farfadowar tattalin arziki kamar yadda ake fata. Taron ganawar shugabannin kasashen Sin, da Japan da Koriya ta Kudu na wannan karo, ya nuna kyakkyawan fatan kasashen uku, ta fuskar habaka hadin gwiwarsu, da kuma daidaito tsakanin kasashen Japan da Koriya ta Kudu, kan manufofinsu masu nasaba da kasar Sin, da sassauta yanayin siyasa a tsakanin kasashen uku.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Rabon Kayayyakin Amfanin Gona Ga Manoman Kaduna 40,000

Next Post

Tabbatar Da Cikakken ’Yancin Kai, Ita Ce Za Ta Kyautata Dangantakar Sin Da Japan Da Korea Ta Kudu

Related

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

2 hours ago
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

4 hours ago
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

4 hours ago
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%
Daga Birnin Sin

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

5 hours ago
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

6 hours ago
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro
Daga Birnin Sin

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

7 hours ago
Next Post
Tabbatar Da Cikakken ’Yancin Kai, Ita Ce Za Ta Kyautata Dangantakar Sin Da Japan Da Korea Ta Kudu

Tabbatar Da Cikakken ’Yancin Kai, Ita Ce Za Ta Kyautata Dangantakar Sin Da Japan Da Korea Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.