• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Arewa Za Su Ware Kaso 5 Na Kasafi Don Taimaka Wa ‘Yan Gudun Hijira

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnonin jihohin Adamawa, Benuwai, Borno da Yobe sun sha alwashin ware kaso sama da biyar daga cikin kasafin kudin jihohinsu domin taimaka wa rayuwar ‘yan gudun hijira sama da miliyan hudu da suke zaman neman mafaka a jihohinsu.

Gwamnonin sun sha alwashin ne yayin wani taron kaddamar da shiri na musamman domin nemi mafita mai dorewa kan halin da ‘yan gudun hijira ke ciki da ya gudana a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

  • Taron Gwamnonin Arewa Maso Gabas Karo Na 10, Me Ya Kamata Ku Sani?
  • Mun Rage Barazanar Ƴan Bindiga Da 70% A Jihar Katsina – Gwamna Radda

Da take magana a yayin taron ta yanar gizo, mataimakiyar babban sakataren majalisar dinkin duniya, Amina Mohammed, ta ce lalubo bakin zaren shawo kan matsalolin na ‘yan gudun hijira na daga cikin muhimman abubuwan da ya kamata Nijeriya ta sanya a gaba kuma ita kanta majalisar dinkin duniya ta damu da lamarin.

Ta lura kan cewa adadin ‘yan gudun hijira ya ninku a cikin shekaru goma da ya kai kusan mutum miliyan 76 da suke halin gudun hijira a fadin duniya.

“Sama da ‘yan Nijeriya miliyan hudu na neman mafita zuwa inda aka tilasta musu yin kaura na dole,” ta ce, tsarin a matakin farko zai ba da mafita kan yadda za a nemi hanyoyin magance matsalolin da suka shafi na mutanen.

Labarai Masu Nasaba

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Tun da farko a jawabinsa, mukaddashin babban sakataren majalisar dinkin duniya kuma mashawarci kan nemo mafita mai dorewa, Mista Robert Piper, ya jinjina wa irin azamar gwamnatin Nijeriya da shugabanninta wajen ganin sun zama kasa ta farko a cikin kasashe 15 wajen kaddamar da shirin neman mafita mai dorewa ga ‘yan gudun hijira.

Piper ya ce kaddamar da shirin wata alama ce da ke nuni da cewa tabbas ‘yan siyasan da suke kan mulki a yanzu sun himmatu wajen ganin sun taimaka wa ‘yan gudun hijira da nema musu mafita a Nijeriya. Ya ce, dabarbaru da hikimomin yadda za a bi duk suna kunshe cikin shirin.

Shi kuma a nasa bangaren, mataimakin shugaban kasar Nijeriya, Sanata Kashim Shettima, ya yi kira ne na samar da hadin guiwa a duniyance wajen ganin an shawo kan matsalolin ‘yan gudun hijara a Nijeriya.
Ya ce, gwamnatin tarayya ta himmatu ainun wajen ganin ta kyautata da kare rayuwar ‘yan gudun hijira.

Da yake kaddamar da shirin da za a aiwatar a jihohi hudu da suke arewa Adamawa, Benuwai, Borno da Yobe, Shettima ya ce, babu yadda za a yi gwamnati ta dage idonta daga kan ‘yan gudun hijira ko daina damuwa da matsalolinsu, a maimakon hakan ya tabbatar da cewa dole ne a kare rayuwar kowani dan kasa.

Shi kuma a nasa bangaren, gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya ce, gwamnatin jihar a shirye take dari bisa dari wajen aiwatar da shirin da aka tsara domin nemo mafita. Ya ce, gwamnatinsa za ta iya ware kaso mai tsoka fiye da yadda ake tsammani domin nasarar shirin.

Zulum ya ce, gwamnatinsa tana kokarin yadda za su maida ‘yan gudun hijira garuruwansu na asali domin ci gaba da gudanar da harkokin rayuwarsu.

Shi ma gwamna Jihar Benuwai, Hyacinth Alia ya ce, kaddamar da shirin zai taimaka sosai wajen kyautata rayuwa da jin dadin al’umman da suke jiharsa.

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya ce, sun maida hankali wajen gudanar da ayyukan da kai tsaye za su kyautata da inganta rayuwar al’ummarsu, don haka a shirye suke su mara wa shirin kyautata rayuwar ‘yan gudun hijira baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaGwamnonin Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanya Mafi Sauki Da Za A Magance Matsalar Tsaro A Katsina – Gamayyar Kungiyoyin Arewa

Next Post

Na’urorin Kula Da Iyakokin Kasa Za Su Fara Aiki Ba Da Jimawa Ba – Ministan Cikin Gida

Related

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

3 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

4 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da ÆŠansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da ÆŠansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

6 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

7 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da ÆŠansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

8 hours ago
Next Post
iyakokin kasa

Na’urorin Kula Da Iyakokin Kasa Za Su Fara Aiki Ba Da Jimawa Ba – Ministan Cikin Gida

LABARAI MASU NASABA

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.