ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na’urorin Kula Da Iyakokin Kasa Za Su Fara Aiki Ba Da Jimawa Ba – Ministan Cikin Gida

by Khalid Idris Doya
2 years ago
iyakokin kasa

Gwamnatin tarayya ta ce dukkanin iyakokin kasar nan an jibge musu na’urorin sanya ido masu sarrafa kansu domin inganta tsaron kasar da za su fara aiki nan ba da jimawa ba.

Ministan kula da harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, shi ne ya shaida hakan a cikin makon nan a lokacin duba aikin da ake yi na ginawa da zuba kayan aiki a cibiyar kula da ba da umarni na mashiga ta fasahar zamani a filayen jiragen sama da kuma cibiyoyin tattara bayanai na kan iyakoki wadanda suke cikin shalkwatar hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS).

  • Ministan Kudin Zimbabwe Ya Jinjinawa Gudummawar Masu Zuba Jari Daga Sin
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Kira Taron Manema Labarai Game Da Halartar Shugaba Xi Jinping Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Tattauna Hadin-Kan Sin Da Kasashen Larabawa

Ya nuna gamsuwarsa da yadda ake gudanar da aiki mai inganci kuma cikin hanzari, ya lura kan cewa aikin farko na sanya na’uorin sa ido a iyakoki za su kammalu a watan Oktoban 2024.

ADVERTISEMENT

Ya sanar da cewa ginawa da sanya kayan aiki a cibiyar ba da umarnin da kula da ke NIS ya kammalu kaso dari bisa dari, wanda ana jiran kaddamar daga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu zai jagoranta. Ya kuma ce aikin sa ido kan iyakoki na zamani ya kai kaso 60 cikin dari na kammaluwa.

“Muna zaman jiran shugaban kasa ne domin kaddamarwa. TunI muka sanar da shugaban kasa kuma ina farin cikin sanar da ‘yan jarida cewa aikin an kammala shi 100 bisa 100.”

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Tunji-Ojo ya kara da cewa tsarin sa ido kan iyakoki mai amfani da kansa na zamani zai taimaka wajen dakile aikata laifuka a iyakoki da kuma samun damar bibiyar iyakoki tun daga shalkwatar NIS kai tsaye.

Ministan ya jaddada cewa kula da tsaron iyakoki na da muhimmanci kuma na daga cikin muhimman abubuwan da Shugaban Tinubu ba zai yi sako-sako da su ba domin tabbatar da tsaro da kare ‘yan kasa.

Kwanturola janar na hukumar shige da fice, Kemi Nanna Nandap, ta bayyana cewa an horas da jami’ansu yadda za su tafiyar da sabbin na’urorin da ke aiki da kansa, inda ta ce a yanzu haka ma wasu jami’an na samun horo kan hakan.

Nandap ta kara da cewa al’ummomin da suke iyakokin kasar su ma an wayar musu da kai kan irin gudunmawar da ake fatan za su bayar domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba ciki har da bayar da muhimman bayanan da suka dace ga NIS a duk lokacin da bukatar hakan.

iyakokin kasa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
nahcon

NAHCON Ta Karyata Rahoton Bayar Da Abinci Mara Inganci Ga Alhazai A Makkah

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.