• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Hada Kai Domin Yaki Da Shan Miyagun Kwayoyi (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
3 years ago
in Bakon Marubuci
0
A Hada Kai Domin Yaki Da Shan Miyagun Kwayoyi (Ra’ayinmu)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 26 ga watan Yuni na kowacce shekara ne Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin fadakar da al’umma a kan barnar da shaye-shayen miyagun kwayoyi ke yi ga rayuwar al’umma musamman matasa, barna ya munana, ta haka ake saran al’umma za su fahimci barnar da matsalar da ke tattare da nomawa da safarar muggan kwayoyi a cikin al’umma.

Abin takaici shi ne wannan gangamin na wannan shekarar yana zuwa ne a daidai lokacin da mu’amala da kwayoyi a tsakanin matasanmu take dada karuwa ne a kullum. Kidididgar da aka yi a shekarar 2019, ta nuna cewa, an fi shan tabar wiwi a tsakanin matasan inda aka gano cewa, akalla ‘yan Nijeriya fiye da Miliyan 10.6 ke shan tabar wiwi, inda wasu na fara shan tabar ne tun suna shekara 19 a duniya.

  • NDLEA Ta Damke Wata Mata Za Ta Yi Safarar Miyagun Kwayoyi Zuwa Oman

Haka kuma binciken wanda kungiyar ‘Global Drug Surbey’ ta gudanar ya nuna cewa, an fi shan kwayar ne a yankin Afrika ta Yamma.

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta tabbatar da cewa, tabar wiwi ce aka fi sha a yankin Afirka, inda aka samu kashi 5.2 zuwa 13.5 na masu shan tabar a yankin Afirka mafi yawansu kuma na yankin Afirka ta Yanma ne, ana kuma iya cewa, al’amarin kwayoyin ya yi kamari a Nijeriya fiye da wata kasa a Afirka.

Haka kuma a binciken da kungiyar ‘National Drug Use and Health Surbey’ ta gudanar a shekarar 2018, ta gano cewa, fiye da mutum 376,000 na cikin tsananin mu’amala da kwayoyi, inda daya daga cikin mutum 5 zaka samu daya yana amfani da kwayoyi da ake tsira wa da allura. Fiye da mutum 80,000 da ke amfani da allurar wajen zukar kwayoyin na fuskantar yada cututtuka kamar su Kanjamar da cutar hanta.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Babu kokwanto, nada Birgediya Janar Buba Marwa a mastayin shugaban Hukumar Yaki da Safarar Miyagun Kwayoyi ya taimaka kwarai wajen zaburar da hukumar a yakin da ake yi da safarar miyagun kwayoyi a Nijeriya.

Yana da muhimmanci a fahimci cewa a cikin wata 17 da suka wuce an samu nasarar kama masu safarar miyagun kwayoyi fiye da 17, 647 an kuma samu nasarar garkame manyan diloli masu safara kwayoyin 10, haka nan kuma hukumar ta samu nasarar zartar da hukunci a kan mutum 2,369 an kuma samu nasarar warkar da masu mu’amala da miyagun kwayoyin fiye 11,000 a daidai wanna lokacin da ake magana.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, ya zama dole a yi nasara a yakin da ake fuskanta a kan safara da amfani da miyagun kwayoyi saboda dangantakar miyagun kwayoyi da matsalar tsaro.

Idan za a iya tunawa a shekarar 2020, mai ba shugaban kasa shawara a kan harkar tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno (mai ritaya) ya danganta yawaitar matsalar a kasar nan da yadda ake mu’amala da miyagun kwayoyi, ya kuma ce, lallai abin ya zama abin tayar da hankali.

A halin yanzu an dora Nijeriya a matsayin kasar da ta fi hatsari a kan ayyukan ‘yan ta’adda. A bin takaicin shi ne yadda harkokin ‘yan ta’adda ke kara karuwa a kullum suna cin karen su babu babbaka, duk da cewa, babu wani shashe na duniya da ya tsira daga abubuwan da suka shafi ayyukan ‘yan ta’adda amma lamarin Nijeriya yana da ban tsoro.

Don nuna jajircewarsa a kan yaki da miyagun kwayoyi, shugaban kasa Muhammadu Buhari, a shekarar da ta gabata ya kaddamar da shiri na musamman da aka yi wa lakabi da ‘War Against Drug Abuse” (WADA)’ da kuma kundi na musanmman mai suna “National Drug Control Master Plan 2021-2025” na yadda za a fuskanci yaki da miyagun kwayoyi a sasan kasar nan.

Shugaban kasar ya kuma ce, barazanar da miyagun kwayo ke yi wa kasar nan ya fi na ayyukan ta’addanci da ake fuskanta.
Mun amince da bayanin shugaban kasa na cewa, miyagun kwayoyi ya taimaka wajen kara zafafa ayyukan masu garkuwa da mutane da ‘yan ta’adda a sassan Nijeriya, mun kuma amince da irin nasarorin da NDLEA ke samu a yaki da miyagun kwayoyi, muna kuma kira da a kara kaimi wajen zafafa yakin da ake yi da masu safara da mu’amala da miyagun kwayoyi a sassan kasar nan ta haka za a tabbatar da rage lamarin yadda ya kamata.

Wannan yaki na kowa da kowa ne a saboda haka muna kira ga iyalai, makarantu da kungiyoyi masu zaman kansu da sauran al’umma gaba daya su kawo nasu gudummawar don samun nasarar fatattakar masu safarar kwayoyi da masu mu’amala da ita, tare da kuma ba hukumar NDLEA goyon bayan da take bukata gaba daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

Next Post

2023: Jama’a Su Ajiye Jam’iyya Su Zabi Cancanta – Malam Murtala

Related

Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Bakon Marubuci

Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

1 week ago
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan
Bakon Marubuci

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

2 weeks ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

3 weeks ago
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata
Bakon Marubuci

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

3 weeks ago
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
Bakon Marubuci

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

2 months ago
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus
Bakon Marubuci

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

2 months ago
Next Post
2023: Jama’a Su Ajiye Jam’iyya Su Zabi Cancanta – Malam Murtala

2023: Jama'a Su Ajiye Jam'iyya Su Zabi Cancanta - Malam Murtala

LABARAI MASU NASABA

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.