• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Sabuwa: EFCC Ta Buɗe Littafin Kwankwaso

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Wata Sabuwa: EFCC Ta Buɗe Littafin Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC) ta fara bincike kan zargin karkatar da kuɗaɗen yaƙin neman zaɓe da jam’iyyar NNPP ta yi a zaben 2023. Binciken dai ya mayar da hankali ne kan zarge-zargen da ake yi wa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da tawagarsa, musamman gazawar kwamitin ayyuka na jam’iyyar a ƙarƙashin jagorancin Kwankwaso, wajen biyan wakilan jam’iyyar da suka yi aiki a lokacin zaɓen shugaban ƙasa da na gwamna.

EFCC na bin diddigin ikirarin da Kwankwaso da sakatariyarsa, Misis Folashade Aliu, suka yi na karkatar da kuɗaɗen ta hanyar wani asusun kamfen na sirri da kuma bayar da tallafi.

  • Sojojin Nijeriya Na Da Kwarewar Da Za Su Kawo Karshen Matsalar Tsaro –  Kwankwaso
  • APC Ta Zargi Kwankwaso Da Shirya Wa Ganduje Maƙarƙashiya Kafin Zaben 2027

Hukumar EFCC ta gayyaci Comrade Oginni Olaposi Sunday, sakataren jam’iyyar NNPP domin ya tabbatar da waɗannan zarge-zarge. A cewar wasu majiyoyi, koken Oginni ya shafi manyan masu sa hannun a asusun bankin NNPP da suka haɗa da Farfesa Rufa’i Alkali, Abba Kawu, da Dipo Olayokun.

EFCC na iya tsawaita bincikenta don bincikar Olayokun yadda ya tara dukiya da a Abuja cikin kankanin lokaci, wanda hakan ke nuni da cewa za a iya tafka maguɗi a harkar kuɗi da ke da nasaba da rawar da ya taka a matsayinsa na sa mai sa hannu.

Da yake tabbatar da ziyarar da ya kai shelƙwatar EFCC a kwanakin baya, Oginni ya bayyana cewa ya bayar da bayanan da suka dace da kuma ƙarin haske dangane da ƙarar.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Ya yabawa jami’an na EFCC bisa kwarewarsu tare da jaddada ƙudirin hukumar na yaki da cin hanci da rashawa. Yayin da Oginni ya tabbatar da binciken hukumar EFCC, ana sa ran nan ba da daɗewa ba za a gurfanar da Sanata Kwankwaso da sauran masu ruwa da tsaki kan zargin almundahanar Naira biliyan 2.5.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EFCCKwankwasoNNPPsiyasar Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sarki Sanusi Ya Naɗa Dagacin Janguza Duk Da Rikicin Masarautar Kano

Next Post

Rundunar PLA Za Ta Shiga Atisayen Hadin Gwiwa A Najeriya

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

11 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 day ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Rundunar PLA Za Ta Shiga Atisayen Hadin Gwiwa A Najeriya

Rundunar PLA Za Ta Shiga Atisayen Hadin Gwiwa A Najeriya

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
EFCC

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.