• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Kasashen Larabawa Za Su Gaggauta Aikin Kafa Al’umma Mai Makomar Bai Daya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Kasashen Larabawa Za Su Gaggauta Aikin Kafa Al’umma Mai Makomar Bai Daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci bikin bude taron ministoci karo na 10 na dandalin tattauna hadin kan Sin da kasashen Larabawa a jiya Alhamis, inda ya sanar da cewa, kasar Sin za ta kira taron koli karo na 2 tsakanin Sin da kasashen Larabawa a shekarar 2026, kuma tabbas, zai kasance sabon babin dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Larabawa. Haka kuma, ya bayyana ra’ayinsa game da yadda za a ci gaba da raya dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu, yayin da ya gabatar da fannoni guda biyar da za su hada kai a nan gaba, domin gaggauta aikin kafa al’umma mai makomar bai daya a tsakanin Sin da kasashen Larabawa.

A bana, ake cika shekaru 20 da kafuwar dandalin tattauna hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Larabawa. Cikin shekaru 20 da suka gabata, bangarorin biyu sun raya dangantakar dake tsakaninsu inda ya zama abin koyi ta fuskar hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Yanzu, ana aiwatar da shirin “Ziri daya da hanya daya” a cikin kasashen Larabawa 22, lamarin da ya tallafawa al’ummomin bangarorin biyu kimanin biliyan 2.

  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Tunisia Kais Saied
  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Tunisia Kais Saied

Kuma an lura cewa, a wannan karo, shugabannin kasashe 4 da suka hada da Bahrain, da Masar, da Tunisiya, da Hadaddiyar Daular Larabawa wato UAE, sun halarci bikin bude taron ministocin. Dangane da wannan lamari, Jaridar Arab Weekly ta fidda wani sharhi dake cewa, halartar shugabannin kasashen hudu taron, ya nuna jagorancin shugabannin Sin da kasashen Larabawa kan hadin gwiwar dake tsakaninsu, ya kuma nuna aniya da fatan shugabannin Sin da Kasashen Larabawa ta karfafa hadin gwiwarsu da kuma raya dangantakar dake tsakaninsu zuwa sabon matsayi. A yayin taron na wannan karo, an kuma gabatar da sanarwar hadin gwiwa ta Sin da kasashen Larabawa game da batun Falesdinu, inda aka yi kiran kawo karshen riciki a yankin Gaza, da kuma warware matsalar daga dukkanin fannoni, kuma bisa adalci.

Taron na wannan karo ya kasance sabon mafari ga kasar Sin da kasashen Larabawa, don haka ya kamata su dauki matakai masu dacewa yayin aiwatar da ayyukansu yadda ya kamata, domin shimfida zaman lafiya da zaman karko ga duniyarmu dake cikin halin sauye-sauye. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Fasahar ‘HereafterAI’ Ke Ba Da Damar Magana Da Muryar Mutum Bayan Mutuwarsa

Next Post

Hanyar Ci Gaba Da Gwamnatin Tinubu Za Ta Bi, Ba Takure Tunani Wuri Guda Ba – Obasanjo

Related

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

13 hours ago
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika
Daga Birnin Sin

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

14 hours ago
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

15 hours ago
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

16 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

17 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

18 hours ago
Next Post
Obasanjo

Hanyar Ci Gaba Da Gwamnatin Tinubu Za Ta Bi, Ba Takure Tunani Wuri Guda Ba – Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.