ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyar Ci Gaba Da Gwamnatin Tinubu Za Ta Bi, Ba Takure Tunani Wuri Guda Ba – Obasanjo

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Obasanjo

Tsohon shugaban kasar Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya caccaki manufofi da tsare-tsaren gwamnatin Shugaban kasa, Bola Tinubu kan lamuran da suka shafi tsaro da tattalin arziki, yana mai cewa, gwamnati mai ci ba ta daura turbar tafiyar da harkokin mulki yadda ya kamata ba.

Baro-baro ya bayyana cire tallafin man fetur wanda ya janyo cikas wajen huldar kai tsaye tsakanin ‘yan kasuwancin canjin da kuma canjin kudaden kasar waje a hukumance, gami da tsoma baki dumu-dumu kan juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar da ke makwafta da Nijeriya, wato Jamhuriyyar Nijar.

  • Rikicin Masarautar Kano: Lauyoyi Da Alƙalai Sun Tozarta Ɓangaren Shari’a – Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi
  • Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara

Obasanjo ya lura kan cewa matakai uku da gwamnatin Tinubu ta dauka, biyu daga ciki sun kasance kusan ma wajibi ne a dauki matakin hakan, amma wajen aiwatar da su ne aka tafka kurakuran da suka jefa sashin tattalin arzikin kasar cikin halin ni-‘yasu.

ADVERTISEMENT

Ya kuma bayyana cewar kasar nan ba za ta kai zuwa matakin da ake fatan zuwa ba har sai shugabanninta sun bijiro da ajandan ci gaba na tsawon shekara 25 da dokar da ya samu goyon bayan ‘yan majalisun tarayya da na jihohi,

A wata sanarwa da ya fitar a Abeokuta, babban birnin Jihar Osun dauke da sanya hannun hadiminsa a bangaren yada labarai, Kehinde Akinyemi, tsohon shugaban ya ce tabbas gwamnatin yanzu ba ta dauki lamarin tattalin arziki ta hanyoyin da suka dace ba, wanda hakan ne ya janyo ‘yan kasar ke cikin ukuba kuma ake ta samun koma-bayan kan faduwar darajar naira.

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Sanarwar ta yi bayanin cewa Obasanjo wanda ya yi wadannan maganganun a wajen wani taron ci gaban Nijeriya, hanyoyin da gwamnati ke bi da ba su kamata ba wajen tafiyar da tattalin arziki da tsaro da ya gudana Paul Aje Collokuium (tPAC) da ke Abuja.

Obasanjo ya kuma soki wadanda suke caccakar matakinsa da ya dauka kan garanbawul ga matatar man Fatakwal a Jihar Ribas, ya misalta masu kushen da cewa masu yunkurin yaudaran jama’a ne.

Ya ce, masu irin wannan kushen sun kasa tuna irin kokarin da aka yi a shekarar 2007 na ganin an gyara matuntun mai da ya yi da kuma irin zurfin tunani da ya dauka kafin aiwatar da shawara ta karshe.

A cewarsa, hanyar ci gaba shi ne zurfun tunani da aiki tukuru da gwamnati za ta yi, ba wai ta takure tunani waje guda da daukan matakan na ‘yan kankanin lokaci ba.

Obasanjo
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Hakkin Bil Adam Gata Ne Ga Wasu A Amurka Karkashin Ra’ayin Wariyar Launin Fata

Hakkin Bil Adam Gata Ne Ga Wasu A Amurka Karkashin Ra’ayin Wariyar Launin Fata

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.