• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarar Yaki Da Hanci A Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Nasarar Yaki Da Hanci A Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yaki da cin hanci shi ne babban kudurin da shugabannin kasar Sin suka sa a gaba,musamman bayan babban taro karo na 18 na wakilan jam’iyyar kwaminis mai mulki a kasar da aka gudanar a shekarar 2012, inda suka zage dantse wajen yaki da cin hanci a bisa doron halaccin tsarin siyasa.

Gwamanti mai ci a yanzu karkashin jagorancin shugaba Xi Jinping duk da irin kalubalen da take fuskanta ta sami gagarumar nasara wajen fito da sabuwar dokar daukar hukunci mai tsanani ga duk wata harkar cin hanci da karbar rashawa a kasar.

  • Shugaban Zimbabwe Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Kammala Sabon Ginin Majalisar Dokokin Kasar

A yunkurin kawo karshen cin hanci a kasar Sin, gwamnatin kasar ta yi nazari na tsanaki domin gano dalilai da kuma illar da cin hanci da rashawa suka yiwa kasar.

Irin matakin da kasar Sin ta dauka na kawo karshen cin hanci sun hada da kafa hukumomin yaki da cin hanci da rashawa tare da yin hukunci mai tsanani ga duk wanda aka samu da aikata laifin cin hanci.

Hakika a wannan mataki kwalliya ta biya kudin sabulu domin gwamnati da jam’iyyar Kwaminisanci mai mulki sun hada karfi wuri guda wajen yakar cin hanci da kuma wanzar da hukunci kan doron shari’a ta yadda aka sami tsabtatacciyar gwamnati wadda babu bara gurbi a cikinta.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Irin matakan da gwamnatin ta Xi Jinping ta dauka da zummar cika burinta na kakkabe rashawa su ne kafa babban kwamitin binciko laifin cin rashawa na kasar.

Wannan kwamiti na binciko laifin cin rashawa ya zamanto kan gaba wajen gano ayyukan rashawa a kasar, inda ya binciko laifukan cin hanci da rashawa da kuma hukunta wadanda ke da hannu a ciki sama da mutane miliyan hudu a kowane matakin mukami na gwamnati.

Abin sha’awa a nan shi ne wannan kwamiti na binciko aikita laifin rashawa yana gabatar da wani shiri na kashin kansa mai suna “ba gudu babu ja baya wajen kauda rashawa” wato “zero tolerance” a Turance. Manufar wannan shiri ita ce nunawa ’yan kasa irin nasarar da kwamitin yake samu na yaki da karbar shawara tare da fallasa duk wani hamshakin gwamnati da aka samu da aikata laifin cin rashawa komai girman mukaminsa.

A rahoton kwamitin na shekarar 2018 zuwa ta 2020, kwamitin ya bayyana cewa ya yi nasarar kamo ’yan kasar da suka tsere zuwa kasashen ketare kimanin 3848, haka kuma an sami nasarar dawo da kusan biliyan goma na kudin kasar da aka yi awon gaba da su.

A hannu guda hukumar ta dauki matakan kau da cin hanci a kasar ta hanyoyi da dama, kadan daga ciki su ne, na daya, gwamantin kasar Sin ta bijiro da shirin ilmantar da ma’aikatan gwamnati kan rikon amana da kishin kasa ta yadda cin hanci da rashawa ba zai sami gurbi a cikin aikin gwamnati ba.

A dai wannan gabar gwamnatin ta tsara jadawalin ilimi a manhajar manyan makarantu na jami’o’i, makarantun sakandare da kuma makarantun firamare.

Duk wadannan matakai an dauke su ne da zimmar fahimtar da ‘yan kasa illar cin hanci da rashawa da kuma yadda suke rugurguza manufofin gwamnati na kyautata rayuwar ‘yan kasa.

Babu shakka irin wannan matakai da kasar Sin ta dauka sun taimaka kwarai da gaske wajen manufofin gwamnati na samar da rayuwa mai inganci ga ‘yan kasa.

Abin alfahari ga kasar ta Sin a yau shi ne yadda kasar ta yi bikin fidda miliyoyin ‘ya’yanta daga kangin talauci da fatara gami da kuma inganta rayuwar mazauna yankunan karkara, inda aka samar musu mazauni na zamani mai dauke da kayan alatu na more rayuwa kamar a manyan birane na kasar ta Sin.

A karshe wannan mataki na kauda cin hanci da rashawa da gwamnatin kasar Sin ta dauka karkashin jagorancin shugaba Xi Jinping ya jawowa kasar ta Sin kima a idon sauran kasashen duniya, haka kuma irin ci gaban da kasar ta Sin ta samu a bangaren kimiyya da fasahar zamani ta zamanto gagara gasa a fagen kere-kere a duk fadin duniya. (Garba Shu’aibu Dakata)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Maye Sunan Mohammed Abacha Da Sadiq Wali A Matsayin Dan Takarar PDP A Kano

Next Post

Tinubu Da Gwamnonin Kudu Ba Su Halarci Taron Da Buhari Ya Yi Game Da APC Ba

Related

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

11 hours ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

12 hours ago
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

14 hours ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

1 day ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

1 day ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

1 day ago
Next Post
Tinubu Da Gwamnonin Kudu Ba Su Halarci Taron Da Buhari Ya Yi Game Da APC Ba

Tinubu Da Gwamnonin Kudu Ba Su Halarci Taron Da Buhari Ya Yi Game Da APC Ba

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.