• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumonin Saudiya Sun Tsananta Fatattakar Bakin Haure

by Bello Hamza
1 year ago
in Kasashen Ketare, Labarai
0
Hukumonin Saudiya Sun Tsananta Fatattakar Bakin Haure
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga dukkan alamu hukumomin Saudiya sun samar da matakai na hana bakin haure da aka fi sani da Takari sakat a yayin gudanar da aikin hajjin bana na 2024.

Wakilinmu ya lura cewa, ‘yan Nijeriya maza da mata, wasu ma a kasar aka haifi iyayen su suna gudanar da harkokin saye da sayarwa na abinci da tufafi a kofofin Otal-otal da masallatan unguwannin da kuma hanyoyin zuwa masallacin Harami.

  • Hajjin Bana: Saudiyya Ta Ba NAHCON Izinin Buɗe Asibitoci Biyu A Kasar
  • Maniyyata Miliyan 1.2 Sun Iso Saudiyya Domin Hajjin Bana – Ma’aikatar Hajji Da Umrah

A wannan shekarar bayan katin shaida na NSUK da aka bukaci kowanne Alhaji ya makala a wuya a yayin zirga zirgarsa a garin Makka domin gane Alhajin gaskiya da na bogi, Askarawa suna sintiri a kai a kai suna fattakar bakin hauren, “Za ka ga sun rungumi buhunan kayan da suke sayarwa suna gudu, abin gwanin ban tausayi”, in ji Alhaji Bello Bala Bungudu.

Hukumar kasar Saudiyya ta haramta wa duk wanda ba shi da izinin gudanar da aikin hajji shiga garin Makka ko da kuwa dan kasar ne, inda ta ayyana hukuncin daurin shekara 6 ga duk wanda aka kama da irin wannan laifin.

A tsokacinsa, wani dan jarida da ya dade yana shiga kasar Saudiya, Alhaji Kabir Yusuf, ya ce, yawancin irin wadannan mutanen suna shigowa ne da cikakken izini, ta hanyar zuwa Umara ko aikin Hajj ko kuma ta hannun kamfanonin daukar ma’aikata masu daukar ‘yan aikatau, amma da zaran takardar izinin zaman su ya kare sai su ci gaba da kulli kucciya tsakaninsu da jami’an tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Ya kara da cewa, a irin wannan ne zaka samu mutum ya yi shekaru a kasar, ya yi aure, ya hayayyafa, shida zuriyyarsa duk suna zama ba bisa ka’ida ba.

Ya ce, duk da halin matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a Nijeriya, ya kamata matasa su yi tunanin irin wulakancin da ake yi wa ‘yan Takari, “ Idan an kama mutum, bayan ya yi zaman gidan yari sai a kwace dukiyarsa a kuma fitar da shi zuwa wata kasar Afirka da karfin tsiya.
A kan haka ya shawarci gwamnati su farfado da tattalin azikin kasa ta yadda rayuwa zai yi dadi a Nijeriya.

Asibitocin NAHCON Sun Fara Aiki A Makkah
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta sanar da samun amincewar Ma’aikatar Lafiya ta Kasar Saudiya ta bude cibiyoyin lafiya guda biyu a garin Makkah domin aikin kula da lafiyar Alhazai a garin Makkah.

Ma’aikatar Lafiya ta kasar Saudiyya ta mika sakon ne ta hannun Kungiyar Kwararrun Likitocinta da ke aikin kula lafiya a karkashin kamfanin Ithra Alkhair, a cikin wata takardar da ta aike wa ofishin Hukumar NAHCON da ke birnin na Makkah. Tuni kuma suka fara aiki gadangadan.

Bayanin da ke kunshe a cikin takardar ya nuna cewa manyan asibitocin guda biyu wadanda za a bude za su kasance ne a unguwannin da ke Masfala/Kudai da yankin Shari’e Al-Mansour, za kuma su ci gaba da aiki a matsayin manyan asibitoci, za kuma su yi jinyar manya da kananan matsalolin lafiya da ka iya tasowa daga Alhazai a zaman su na Makkah.

Dakta Abubakar Adamu Isma’eel, Shugaban bangaren Ma’aikatan Lafiya na NAHCON masu aiki a a cikin garin Makkah a wannan shekarar (2024) ne ya karbi takardar amincewar a madadin hukumar Alhazai na Nijeriya.

A jawabinsa Dakta Abubakar ya bayyana cewa, a halin yanzu suna da karin wasu asibitoci uku da suke jiran a basu amincewar gudanar da aiki nan gaba kadan, wanda haka zai samu damar bayar da cikakkiyar kulawa ga dukkan Alhazan Nijeriya.

Asibitocin guda uku da za a bude a nan gaba za su samu cikakkiyar amincewar yin aiki kamar yadda ya kamata.

A ana sa ran asibitocin za su yi aiki ne a masaukan Alhazai guda uku da suka hada masaukan Alhazan Nasarawa, Ogun, Oyo da kuma Masaukan Alhazan Jihar Borno.

Ya kuma kara da cewa za a samar da na’urar GPS na wuraren da Assibitocin suke nan da dan lokaci domin al’umma su samun saukin gane asibitocin.

Tuni dai Hukumar NAHCON ta tura tawagar kwararrun likitocin da ke shirin aiki tukuru domin kulawa da lafiyar Alhazan Nijeriya. Don haka Hukumar ta nemi hadin kan Alhazan Nijeriya domin samun nasarar wannan aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HajjiSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Adawa Da Aniyar Amurka Ta Sayarwa Yankin Taiwan Makamai

Next Post

Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

Related

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

1 minute ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

2 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

3 hours ago
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

12 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

13 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

14 hours ago
Next Post
Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.