ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumonin Saudiya Sun Tsananta Fatattakar Bakin Haure

by Bello Hamza
2 years ago
Saudiya

Daga dukkan alamu hukumomin Saudiya sun samar da matakai na hana bakin haure da aka fi sani da Takari sakat a yayin gudanar da aikin hajjin bana na 2024.

Wakilinmu ya lura cewa, ‘yan Nijeriya maza da mata, wasu ma a kasar aka haifi iyayen su suna gudanar da harkokin saye da sayarwa na abinci da tufafi a kofofin Otal-otal da masallatan unguwannin da kuma hanyoyin zuwa masallacin Harami.

  • Hajjin Bana: Saudiyya Ta Ba NAHCON Izinin Buɗe Asibitoci Biyu A Kasar
  • Maniyyata Miliyan 1.2 Sun Iso Saudiyya Domin Hajjin Bana – Ma’aikatar Hajji Da Umrah

A wannan shekarar bayan katin shaida na NSUK da aka bukaci kowanne Alhaji ya makala a wuya a yayin zirga zirgarsa a garin Makka domin gane Alhajin gaskiya da na bogi, Askarawa suna sintiri a kai a kai suna fattakar bakin hauren, “Za ka ga sun rungumi buhunan kayan da suke sayarwa suna gudu, abin gwanin ban tausayi”, in ji Alhaji Bello Bala Bungudu.

ADVERTISEMENT

Hukumar kasar Saudiyya ta haramta wa duk wanda ba shi da izinin gudanar da aikin hajji shiga garin Makka ko da kuwa dan kasar ne, inda ta ayyana hukuncin daurin shekara 6 ga duk wanda aka kama da irin wannan laifin.

A tsokacinsa, wani dan jarida da ya dade yana shiga kasar Saudiya, Alhaji Kabir Yusuf, ya ce, yawancin irin wadannan mutanen suna shigowa ne da cikakken izini, ta hanyar zuwa Umara ko aikin Hajj ko kuma ta hannun kamfanonin daukar ma’aikata masu daukar ‘yan aikatau, amma da zaran takardar izinin zaman su ya kare sai su ci gaba da kulli kucciya tsakaninsu da jami’an tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ya kara da cewa, a irin wannan ne zaka samu mutum ya yi shekaru a kasar, ya yi aure, ya hayayyafa, shida zuriyyarsa duk suna zama ba bisa ka’ida ba.

Ya ce, duk da halin matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a Nijeriya, ya kamata matasa su yi tunanin irin wulakancin da ake yi wa ‘yan Takari, “ Idan an kama mutum, bayan ya yi zaman gidan yari sai a kwace dukiyarsa a kuma fitar da shi zuwa wata kasar Afirka da karfin tsiya.
A kan haka ya shawarci gwamnati su farfado da tattalin azikin kasa ta yadda rayuwa zai yi dadi a Nijeriya.

Asibitocin NAHCON Sun Fara Aiki A Makkah
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta sanar da samun amincewar Ma’aikatar Lafiya ta Kasar Saudiya ta bude cibiyoyin lafiya guda biyu a garin Makkah domin aikin kula da lafiyar Alhazai a garin Makkah.

Ma’aikatar Lafiya ta kasar Saudiyya ta mika sakon ne ta hannun Kungiyar Kwararrun Likitocinta da ke aikin kula lafiya a karkashin kamfanin Ithra Alkhair, a cikin wata takardar da ta aike wa ofishin Hukumar NAHCON da ke birnin na Makkah. Tuni kuma suka fara aiki gadangadan.

Bayanin da ke kunshe a cikin takardar ya nuna cewa manyan asibitocin guda biyu wadanda za a bude za su kasance ne a unguwannin da ke Masfala/Kudai da yankin Shari’e Al-Mansour, za kuma su ci gaba da aiki a matsayin manyan asibitoci, za kuma su yi jinyar manya da kananan matsalolin lafiya da ka iya tasowa daga Alhazai a zaman su na Makkah.

Dakta Abubakar Adamu Isma’eel, Shugaban bangaren Ma’aikatan Lafiya na NAHCON masu aiki a a cikin garin Makkah a wannan shekarar (2024) ne ya karbi takardar amincewar a madadin hukumar Alhazai na Nijeriya.

A jawabinsa Dakta Abubakar ya bayyana cewa, a halin yanzu suna da karin wasu asibitoci uku da suke jiran a basu amincewar gudanar da aiki nan gaba kadan, wanda haka zai samu damar bayar da cikakkiyar kulawa ga dukkan Alhazan Nijeriya.

Asibitocin guda uku da za a bude a nan gaba za su samu cikakkiyar amincewar yin aiki kamar yadda ya kamata.

A ana sa ran asibitocin za su yi aiki ne a masaukan Alhazai guda uku da suka hada masaukan Alhazan Nasarawa, Ogun, Oyo da kuma Masaukan Alhazan Jihar Borno.

Ya kuma kara da cewa za a samar da na’urar GPS na wuraren da Assibitocin suke nan da dan lokaci domin al’umma su samun saukin gane asibitocin.

Tuni dai Hukumar NAHCON ta tura tawagar kwararrun likitocin da ke shirin aiki tukuru domin kulawa da lafiyar Alhazan Nijeriya. Don haka Hukumar ta nemi hadin kan Alhazan Nijeriya domin samun nasarar wannan aiki.

Saudiya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.