ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumonin Saudiya Sun Tsananta Fatattakar Bakin Haure

by Bello Hamza
2 years ago
Saudiya

Daga dukkan alamu hukumomin Saudiya sun samar da matakai na hana bakin haure da aka fi sani da Takari sakat a yayin gudanar da aikin hajjin bana na 2024.

Wakilinmu ya lura cewa, ‘yan Nijeriya maza da mata, wasu ma a kasar aka haifi iyayen su suna gudanar da harkokin saye da sayarwa na abinci da tufafi a kofofin Otal-otal da masallatan unguwannin da kuma hanyoyin zuwa masallacin Harami.

  • Hajjin Bana: Saudiyya Ta Ba NAHCON Izinin Buɗe Asibitoci Biyu A Kasar
  • Maniyyata Miliyan 1.2 Sun Iso Saudiyya Domin Hajjin Bana – Ma’aikatar Hajji Da Umrah

A wannan shekarar bayan katin shaida na NSUK da aka bukaci kowanne Alhaji ya makala a wuya a yayin zirga zirgarsa a garin Makka domin gane Alhajin gaskiya da na bogi, Askarawa suna sintiri a kai a kai suna fattakar bakin hauren, “Za ka ga sun rungumi buhunan kayan da suke sayarwa suna gudu, abin gwanin ban tausayi”, in ji Alhaji Bello Bala Bungudu.

ADVERTISEMENT

Hukumar kasar Saudiyya ta haramta wa duk wanda ba shi da izinin gudanar da aikin hajji shiga garin Makka ko da kuwa dan kasar ne, inda ta ayyana hukuncin daurin shekara 6 ga duk wanda aka kama da irin wannan laifin.

A tsokacinsa, wani dan jarida da ya dade yana shiga kasar Saudiya, Alhaji Kabir Yusuf, ya ce, yawancin irin wadannan mutanen suna shigowa ne da cikakken izini, ta hanyar zuwa Umara ko aikin Hajj ko kuma ta hannun kamfanonin daukar ma’aikata masu daukar ‘yan aikatau, amma da zaran takardar izinin zaman su ya kare sai su ci gaba da kulli kucciya tsakaninsu da jami’an tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Ya kara da cewa, a irin wannan ne zaka samu mutum ya yi shekaru a kasar, ya yi aure, ya hayayyafa, shida zuriyyarsa duk suna zama ba bisa ka’ida ba.

Ya ce, duk da halin matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a Nijeriya, ya kamata matasa su yi tunanin irin wulakancin da ake yi wa ‘yan Takari, “ Idan an kama mutum, bayan ya yi zaman gidan yari sai a kwace dukiyarsa a kuma fitar da shi zuwa wata kasar Afirka da karfin tsiya.
A kan haka ya shawarci gwamnati su farfado da tattalin azikin kasa ta yadda rayuwa zai yi dadi a Nijeriya.

Asibitocin NAHCON Sun Fara Aiki A Makkah
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta sanar da samun amincewar Ma’aikatar Lafiya ta Kasar Saudiya ta bude cibiyoyin lafiya guda biyu a garin Makkah domin aikin kula da lafiyar Alhazai a garin Makkah.

Ma’aikatar Lafiya ta kasar Saudiyya ta mika sakon ne ta hannun Kungiyar Kwararrun Likitocinta da ke aikin kula lafiya a karkashin kamfanin Ithra Alkhair, a cikin wata takardar da ta aike wa ofishin Hukumar NAHCON da ke birnin na Makkah. Tuni kuma suka fara aiki gadangadan.

Bayanin da ke kunshe a cikin takardar ya nuna cewa manyan asibitocin guda biyu wadanda za a bude za su kasance ne a unguwannin da ke Masfala/Kudai da yankin Shari’e Al-Mansour, za kuma su ci gaba da aiki a matsayin manyan asibitoci, za kuma su yi jinyar manya da kananan matsalolin lafiya da ka iya tasowa daga Alhazai a zaman su na Makkah.

Dakta Abubakar Adamu Isma’eel, Shugaban bangaren Ma’aikatan Lafiya na NAHCON masu aiki a a cikin garin Makkah a wannan shekarar (2024) ne ya karbi takardar amincewar a madadin hukumar Alhazai na Nijeriya.

A jawabinsa Dakta Abubakar ya bayyana cewa, a halin yanzu suna da karin wasu asibitoci uku da suke jiran a basu amincewar gudanar da aiki nan gaba kadan, wanda haka zai samu damar bayar da cikakkiyar kulawa ga dukkan Alhazan Nijeriya.

Asibitocin guda uku da za a bude a nan gaba za su samu cikakkiyar amincewar yin aiki kamar yadda ya kamata.

A ana sa ran asibitocin za su yi aiki ne a masaukan Alhazai guda uku da suka hada masaukan Alhazan Nasarawa, Ogun, Oyo da kuma Masaukan Alhazan Jihar Borno.

Ya kuma kara da cewa za a samar da na’urar GPS na wuraren da Assibitocin suke nan da dan lokaci domin al’umma su samun saukin gane asibitocin.

Tuni dai Hukumar NAHCON ta tura tawagar kwararrun likitocin da ke shirin aiki tukuru domin kulawa da lafiyar Alhazan Nijeriya. Don haka Hukumar ta nemi hadin kan Alhazan Nijeriya domin samun nasarar wannan aiki.

Saudiya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.