ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Gwamnati

A wani yunkuri na ceto kananan hukumomi daga dabaibayin gwamnoni, gwamnatin tarayya ta maka daukacin gwamnonin kasar nan 36 a gaban kotun koli na neman a sakar wa kananan hukumomi mara su ci gashin kansu.

Karamar hukuma ita ce gwamnati mafi kusa da jama’a, kuma ita ke bunkasa al’umma a matakin farko. Sai dai kuma, ingantaccen shugabanci a kananan hukumomi ya gamu da cikas sakamakon irin dabaibayin da gwamnonin jihohi ke musu.

  • Karin Albashi Ya Zama Karfen Kafa A Nijeriya
  • Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Naira 62,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi 

Kudaden kananan hukumomi a asusun tarayya da ake biya duk wata suna zuwa ne daga gwamnatocin jihohinsu.

ADVERTISEMENT

A cikin karar mai lamba SC/CB/343/2024, da babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a, Prince Lateef Fagbemi, ya shigar, gwamnatin tarayya tana neman a bai wa kananan hukumomi cikkiyar ‘yan ci a kasan a matsinsu na mataki na uku na gwamnati.

Ta kuma bukaci kotun kolin da ta bayar da umarni tare da haramta wa gwamnonin jihohi rusa shugabannin kananan hukumomin da aka zaba ba da kuma bayar da umarnin bayan kudaden kananan hukumomi kai tsaye ga asusunsu daidai da yadda kundin tsarin mulki ya tanada ba a asusun hadin gwiwa ba da gwamnoni suka kirkira ba bisa ka’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

A karar da gwamnatin tarayya ta shigar, gwamnatin tarayya na bukatar kotun koli ta bayar da umarni na dakatar da gwamnonin ci gaba da kafa kwamitocin rikon kwarya da za su tafiyar da al’amuran kananan hukumomi wanda ya saba wa tsarin mulkin dimokuradiyya da aka amince da shi.

Haka kuma gwamnatin tarayya ta yi ikirarin cewa Nijeriya a matsayinta ta tarayya, ita ce ta kirkiro kundin tsarin mulki na 1999, wadda aka yi wa kwaskwarima, inda shugaban kasa, a matsayinsa na shugaban gwamnatin tarayya, ya rantse da cewa zai tabbatar da bin tsarin kundin mulki.

Tun bayan zuwan mulkin dimokuradiyya a kasar nan a shekarar 1999, gwamnatocin jihohi ke dabaibaye kananan hukumomi 774 da ke kasar nan.

Ba wai kawai gwamnoni na zabar makusantansu da za su gudanar da harkokin kananan hukumomi ba, har ma suna zayyana yadda za a kashe kudadensu, musamman kason da ake samu daga asusun tarayya.

Wannan lamari yana gunana ne a tsakanin jam’iyyun siyasa masu mulkin gwamnatocin jihohi karkashin kwamishinonin kananan hukumomi da al’amuran sarauta.

Wannan lamari ya sa kananan hukumomi sun rasa ‘yancin kai na gudanar da harkokin kudade da kuma ‘yancin gudanar da ayyuka, wanda ya mayar da su baya da kuma kasa samar da muhimman ayyukan da al’umm za su amfana.

Duk wani yunkuri na bai wa kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kai ta hanyar gyaran kundin tsarin mulkin kasa, gwamnonin sun toshe.

Hatta kotuna da dama, ciki har da kotun koli, sun yi kokarin shiga tsakani a lokuta da dama kan yadda gwamnonin ke nuna halin ko-in-kula da kananan hukumomi ke yi ba tare da cimma wata nasara ba.

Ba wai kawai ba a gudanar da zabuka ba ne ko kuma ana yawan cire shugabanni kananan hukumomi da kansiloli kadai, ana yawan kafa kwamitocin riko domin gudanar da harkokin kananan hukumomi duk saboda kudaden shiga da suke samu.

A yayin da ake ci gaba da sauraren karar a makon da ya gabata, kwamitin alkalai guda bakwai na kotun kolin karkashin jagorancin mai shari’a Garba Lawal, ya umarci gwamnonin wanda babban lauyoyin jihohi suka wakilta da su gabatar da takardar kariyarsu ga wannan sammacin cikin kwanaki bakwai. An dai dage sauraron karar zuwa ranar 13 ga watan Yunin 2024.

Abin jira a gani dai shi ne, yadda gwamnatin tarayya za ta bi sawun karar a lokacin da kotun koli za ta yanke hukunci ko dai ta samu nasara ko akashin haka.

Gwamnati
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.