• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mbappe Zai Sa Riga Mai Lamba 9 A Sabuwar Kungiyarsa

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Mbappe Zai Sa Riga Mai Lamba 9 A Sabuwar Kungiyarsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon dan wasan Real Madrid, Kylian Mbappe, ya saka hannu kan kwantiragin komawa Real Madrid daga Paris St-Germain, idan yarjejeniyarsa ta kare ranar 30 ga watan Yuni.

Tun cikin watan Fabrairu dan wasan na tawagar Faransa ya amince baka da baka da cewar zai koma Sifaniya, sannan cikin watan Mayu aka sanar da zai bar PSG a karshen kakar nan.

  • Mbappe Ya Amince Ya Koma Real Madrid Akan Kwantiragin Shekaru 5 A Karshen Kakar Wasa Ta Bana
  • Wannan Ita Ce Shekarata Ta Karshe A PSG —Mbappe

Mbappe mai shekara 25 a duniya ya saka hannun kan kunshin yarjejeniyar da Real Madrid ta gabatar masa, wanda zai koma Sifaniya ranar 1 ga watan Yuli da za a bude kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a La Liga.

Tuni Real Madrid ta sanar da labarin kammala kulla kwantiragi da Mbappe na tsawon shekara biyar kuma a nan gaba ne kungiyar za ta gabatar da shi gaban magoya baya a Bernabeu kafin fara Euro 2024. Mbappe ya lashe kofin duniya a 2018, kuma shi ne kan gaba a yawan cin kwallaye a PSG mai 256 a raga, tun bayan da ya koma kungiyar aro daga kungiyar Monaco a shekarar 2017.

Ya amince da yarjejeniyar da za ta kare a Real zuwa karshen 2029, sannan kuma zai dinga karbar albashin fam miliyan £12.8m a kowacce kakar wasa da karin ladan £128m da za a biya cikin shekara biyar, kuma zai rike kudin tallace-tallacensa. Sannan zai samu damar buga wasa tare da dan wasa Luca Modric, yayin da dan kwallon Croatia zai kara sa hannu kan yarjejeniyar kakar wasa guda daya a Real Madrid.

Labarai Masu Nasaba

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

Modric, mai shekara 38, ya shiga wasa daga baya ranar Asabar da Real Madrid ta lashe Zakarun Turai na 15 jimilla, bayan da ta doke Borussia Dortmund a Wembley.

Kwantiragin tsohon dan wasan Tottenham din zai kare a karshen watan nan a Real Madrid, amma ana sa ran za a tsawaita masa kaka daya kamar yadda shugaban gudanarwar kungiyar Florentino Perez ya bayyana.

Real Madrid ce ta lashe gasar La Liga na bana kuma na 36 jimilla da tazarar maki 10 tsakaninta da abokiyar hamayyarta wato Barcelona, wadda ta yi ta ukun teburin babbar gasar ta 2023 zuwa 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MadridMbappePSGReal Madrid
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabar ICRC: Aikin Jin Kai Mataki Ne Na Farko Da Ake Bukata Don Shimfida Zaman Lafiya

Next Post

Bayan Rasa Kujerar Minista Da Wata 10, Shetti Ta Yi Aure

Related

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

1 day ago
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana
Wasanni

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

1 day ago
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya FarfaÉ—o Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya FarfaÉ—o Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

2 days ago
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo
Wasanni

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

4 days ago
Lookman
Wasanni

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

5 days ago
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG
Wasanni

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

1 week ago
Next Post
Bayan Rasa Kujerar Minista Da Wata 10, Shetti Ta Yi Aure

Bayan Rasa Kujerar Minista Da Wata 10, Shetti Ta Yi Aure

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da ÆŠangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da ÆŠangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Mbappe

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.