• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mbappe Zai Sa Riga Mai Lamba 9 A Sabuwar Kungiyarsa

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Mbappe Zai Sa Riga Mai Lamba 9 A Sabuwar Kungiyarsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon dan wasan Real Madrid, Kylian Mbappe, ya saka hannu kan kwantiragin komawa Real Madrid daga Paris St-Germain, idan yarjejeniyarsa ta kare ranar 30 ga watan Yuni.

Tun cikin watan Fabrairu dan wasan na tawagar Faransa ya amince baka da baka da cewar zai koma Sifaniya, sannan cikin watan Mayu aka sanar da zai bar PSG a karshen kakar nan.

  • Mbappe Ya Amince Ya Koma Real Madrid Akan Kwantiragin Shekaru 5 A Karshen Kakar Wasa Ta Bana
  • Wannan Ita Ce Shekarata Ta Karshe A PSG —Mbappe

Mbappe mai shekara 25 a duniya ya saka hannun kan kunshin yarjejeniyar da Real Madrid ta gabatar masa, wanda zai koma Sifaniya ranar 1 ga watan Yuli da za a bude kasuwar cinikayyar ‘yan kwallo a La Liga.

Tuni Real Madrid ta sanar da labarin kammala kulla kwantiragi da Mbappe na tsawon shekara biyar kuma a nan gaba ne kungiyar za ta gabatar da shi gaban magoya baya a Bernabeu kafin fara Euro 2024. Mbappe ya lashe kofin duniya a 2018, kuma shi ne kan gaba a yawan cin kwallaye a PSG mai 256 a raga, tun bayan da ya koma kungiyar aro daga kungiyar Monaco a shekarar 2017.

Ya amince da yarjejeniyar da za ta kare a Real zuwa karshen 2029, sannan kuma zai dinga karbar albashin fam miliyan £12.8m a kowacce kakar wasa da karin ladan £128m da za a biya cikin shekara biyar, kuma zai rike kudin tallace-tallacensa. Sannan zai samu damar buga wasa tare da dan wasa Luca Modric, yayin da dan kwallon Croatia zai kara sa hannu kan yarjejeniyar kakar wasa guda daya a Real Madrid.

Labarai Masu Nasaba

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

Modric, mai shekara 38, ya shiga wasa daga baya ranar Asabar da Real Madrid ta lashe Zakarun Turai na 15 jimilla, bayan da ta doke Borussia Dortmund a Wembley.

Kwantiragin tsohon dan wasan Tottenham din zai kare a karshen watan nan a Real Madrid, amma ana sa ran za a tsawaita masa kaka daya kamar yadda shugaban gudanarwar kungiyar Florentino Perez ya bayyana.

Real Madrid ce ta lashe gasar La Liga na bana kuma na 36 jimilla da tazarar maki 10 tsakaninta da abokiyar hamayyarta wato Barcelona, wadda ta yi ta ukun teburin babbar gasar ta 2023 zuwa 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MadridMbappePSGReal Madrid
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabar ICRC: Aikin Jin Kai Mataki Ne Na Farko Da Ake Bukata Don Shimfida Zaman Lafiya

Next Post

Bayan Rasa Kujerar Minista Da Wata 10, Shetti Ta Yi Aure

Related

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

2 days ago
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique
Wasanni

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

3 days ago
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense
Wasanni

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

4 days ago
Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars
Wasanni

Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars

5 days ago
Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa

5 days ago
Da ÆŠumi-ÆŠumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin
Wasanni

Da ÆŠumi-ÆŠumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

5 days ago
Next Post
Bayan Rasa Kujerar Minista Da Wata 10, Shetti Ta Yi Aure

Bayan Rasa Kujerar Minista Da Wata 10, Shetti Ta Yi Aure

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.