• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS Da Kuma Gana Da Takwarorinsa Na Habasha Da Afirka Ta Kudu

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS Da Kuma Gana Da Takwarorinsa Na Habasha Da Afirka Ta Kudu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya halarci taron ministocin kungiyar BRICS a jiya Litinin a birnin Nizhni Novgorod na kasar Rasha.

Yayin taron, Wang Yi ya ce, hadin gwiwar kasashen BRICS ya gudana cikin sauri da inganci a cikin shekara daya da ta gabata, inda har BRICS ta shigar da sabbin mambobi, matakin da ya bude sabon babin hadin gwiwar kasashe masu tasowa dake dogaro da karfinsu, abin da ya sa BRICS ke kara jan hankalin duniya.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Inganta Tsarin Kamfanoni Na Zamani Mai Halayyar Musamman Ta Sin
  • Kasar Sin Ta Gada Tare Da Raya Al’Adun Da Suka Shafi Bikin Gargajiya Na Duanwu

Wang Yi ya ce, “dole ne mu nace ga tabbatar da adalci da gaskiya, mu bi hanyar da ta dace da yanke shawara yadda ya kamata, duba da cewa ana fuskantar ja-in-ja tsakanin ra’ayin mu’amalar bangarori daban daban a duniya da na babakere, da ma ra’ayin bangarori da na kashin kai.”

Ya kara da cewa ya kamata a yi amfani da tsare-tsare da tasirin siyasar kungiyar yadda ya kamata don mai da BRICS wani sabon tsari mai yakini na hadin kan kasa da kasa da bude kofa dake dogaro da tushen kasuwanni masu saurin ci gaba da karfin kasashe masu tasowa.

Mahalarta taron sun yabawa babban tasiri da ci gaban shigar da sabbin mambobi da BRICS ya samu, inda suke ganin cewa, shigar da karin mambobi cikin kungiyar za ta gaggauta samar da iko tsakanin bangarori da dama a duniya da ingiza doka da odar kasa da kasa mai adalci da daidaito, kuma sun amince da tsarin shigar da kasashen hulda cikin kungiyar, inda kuma aka gabatar da “Hadaddiyar Sanarwa Game Da Ganawar Ministocin Wajen Kasashen BRICS”.

Labarai Masu Nasaba

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Sannan a yayin taron, Wang Yi ya gana da takwaransa na Habasha, Taye Atske Selassie, a birnin Nizhny Novgorod na kasar Rasha.

Da yake bayyana Habasha a matsayin muhimmiyar kasa a nahiyar Afrika, kuma mai masaukin hedkwatar kungiyar Tarayyar Afrika (AU), Wang Yi ya ce, zaman lafiya da kwanciyar hankalin kasar na da muhimmanci ga nahiyar. Ya kara da cewa, a shirye Sin take ta zurfafa abota cikin kowanne yanayi, da fadada hadin gwiwa a bangarori daban daban, da kuma ingiza samun karin nasarori a dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, domin jama’arsu su amfana da su.

A nasa bangare, Taye Atske Selassie ya ce, gwamnati da al’ummar Habasha na maraba da daukaka dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa ta abota bisa manyan tsare-tsare a kowanne yanayi. Ya kara da cewa, kasar Sin ce babbar mai zuba jari a Habasha, haka kuma inda ta fi shigar da kayayyakinta, kana dangantakar dake tsakaninsu ta bunkasa tattalin arziki da kyautata zamantakewar Habasha.

Bugu da kari, Wang Yi ya gana da takwaransa ta Afirka ta kudu Naledi Pandor, a garin Nizhni Novgorod na kasar Rasha.

Yayin zantawar tasu a jiya Talata, Wang Yi ya taya Afirka ta kudu murnar gudanar da babban zaben kasa cikin nasara. Yana mai bayyana yadda Sin ke dora muhimmancin gaske ga ci gaban Afirka ta kudu, a matsayin ta na babbar kasa mai tasowa. Ya ce Sin a shirye take ta yi aiki tukuru tare da sassan kasa da kasa a fannin tsare tsare, da samar da murya mai ma’ana, kuma mai daidaito, game da muhimman batutuwa dake addabar duniya, kamar rikicin Ukraine, kana tana fatan ba da gudummawa ga wanzar da zaman lafiya da daidaito a duniya.

A nata bangare kuwa, Naledi Pandor, cewa ta yi Afirka ta kudu na jinjinawa kokarin kasar Sin, na ganin an warware rikicin Ukraine ta hanyar siyasa, da yayata bukatar dakatar da bude wuta a Gaza. Ta ce Afirka ta kudu a shirye take ta karfafa hadin gwiwa da Sin, karkashin dandalolin kasa da kasa, irin su kungiyar BRICS, da G20, don tabbatar da an cimma nasarar raya ci gaban tsare tsaren da ake gudanarwa karkashin su yadda ya kamata. (Masu Fassarawa: Saminu Alhassam, Fa’iza Mustapha, Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Ƙasa Tinubu Zai Yi Jawabi A Ranar Dimokuraɗiyyar Gobe Laraba

Next Post

Sarkin Kano Na 15 Ya Umarci Hakiman Da Ke Goyon Bayansa Su Halarci Hawan Sallah

Related

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

1 hour ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

2 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

4 hours ago
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157
Daga Birnin Sin

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

5 hours ago
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

1 day ago
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

1 day ago
Next Post
Sarkin Kano Na 15 Ya Umarci Hakiman Da Ke Goyon Bayansa Su Halarci Hawan Sallah

Sarkin Kano Na 15 Ya Umarci Hakiman Da Ke Goyon Bayansa Su Halarci Hawan Sallah

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.