ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS Da Kuma Gana Da Takwarorinsa Na Habasha Da Afirka Ta Kudu

by CGTN Hausa
2 years ago
Kasar sin

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya halarci taron ministocin kungiyar BRICS a jiya Litinin a birnin Nizhni Novgorod na kasar Rasha.

Yayin taron, Wang Yi ya ce, hadin gwiwar kasashen BRICS ya gudana cikin sauri da inganci a cikin shekara daya da ta gabata, inda har BRICS ta shigar da sabbin mambobi, matakin da ya bude sabon babin hadin gwiwar kasashe masu tasowa dake dogaro da karfinsu, abin da ya sa BRICS ke kara jan hankalin duniya.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Inganta Tsarin Kamfanoni Na Zamani Mai Halayyar Musamman Ta Sin
  • Kasar Sin Ta Gada Tare Da Raya Al’Adun Da Suka Shafi Bikin Gargajiya Na Duanwu

Wang Yi ya ce, “dole ne mu nace ga tabbatar da adalci da gaskiya, mu bi hanyar da ta dace da yanke shawara yadda ya kamata, duba da cewa ana fuskantar ja-in-ja tsakanin ra’ayin mu’amalar bangarori daban daban a duniya da na babakere, da ma ra’ayin bangarori da na kashin kai.”

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa ya kamata a yi amfani da tsare-tsare da tasirin siyasar kungiyar yadda ya kamata don mai da BRICS wani sabon tsari mai yakini na hadin kan kasa da kasa da bude kofa dake dogaro da tushen kasuwanni masu saurin ci gaba da karfin kasashe masu tasowa.

Mahalarta taron sun yabawa babban tasiri da ci gaban shigar da sabbin mambobi da BRICS ya samu, inda suke ganin cewa, shigar da karin mambobi cikin kungiyar za ta gaggauta samar da iko tsakanin bangarori da dama a duniya da ingiza doka da odar kasa da kasa mai adalci da daidaito, kuma sun amince da tsarin shigar da kasashen hulda cikin kungiyar, inda kuma aka gabatar da “Hadaddiyar Sanarwa Game Da Ganawar Ministocin Wajen Kasashen BRICS”.

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Sannan a yayin taron, Wang Yi ya gana da takwaransa na Habasha, Taye Atske Selassie, a birnin Nizhny Novgorod na kasar Rasha.

Da yake bayyana Habasha a matsayin muhimmiyar kasa a nahiyar Afrika, kuma mai masaukin hedkwatar kungiyar Tarayyar Afrika (AU), Wang Yi ya ce, zaman lafiya da kwanciyar hankalin kasar na da muhimmanci ga nahiyar. Ya kara da cewa, a shirye Sin take ta zurfafa abota cikin kowanne yanayi, da fadada hadin gwiwa a bangarori daban daban, da kuma ingiza samun karin nasarori a dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, domin jama’arsu su amfana da su.

A nasa bangare, Taye Atske Selassie ya ce, gwamnati da al’ummar Habasha na maraba da daukaka dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa ta abota bisa manyan tsare-tsare a kowanne yanayi. Ya kara da cewa, kasar Sin ce babbar mai zuba jari a Habasha, haka kuma inda ta fi shigar da kayayyakinta, kana dangantakar dake tsakaninsu ta bunkasa tattalin arziki da kyautata zamantakewar Habasha.

Bugu da kari, Wang Yi ya gana da takwaransa ta Afirka ta kudu Naledi Pandor, a garin Nizhni Novgorod na kasar Rasha.

Yayin zantawar tasu a jiya Talata, Wang Yi ya taya Afirka ta kudu murnar gudanar da babban zaben kasa cikin nasara. Yana mai bayyana yadda Sin ke dora muhimmancin gaske ga ci gaban Afirka ta kudu, a matsayin ta na babbar kasa mai tasowa. Ya ce Sin a shirye take ta yi aiki tukuru tare da sassan kasa da kasa a fannin tsare tsare, da samar da murya mai ma’ana, kuma mai daidaito, game da muhimman batutuwa dake addabar duniya, kamar rikicin Ukraine, kana tana fatan ba da gudummawa ga wanzar da zaman lafiya da daidaito a duniya.

A nata bangare kuwa, Naledi Pandor, cewa ta yi Afirka ta kudu na jinjinawa kokarin kasar Sin, na ganin an warware rikicin Ukraine ta hanyar siyasa, da yayata bukatar dakatar da bude wuta a Gaza. Ta ce Afirka ta kudu a shirye take ta karfafa hadin gwiwa da Sin, karkashin dandalolin kasa da kasa, irin su kungiyar BRICS, da G20, don tabbatar da an cimma nasarar raya ci gaban tsare tsaren da ake gudanarwa karkashin su yadda ya kamata. (Masu Fassarawa: Saminu Alhassam, Fa’iza Mustapha, Amina Xu)

Kasar sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Next Post
Sarkin Kano Na 15 Ya Umarci Hakiman Da Ke Goyon Bayansa Su Halarci Hawan Sallah

Sarkin Kano Na 15 Ya Umarci Hakiman Da Ke Goyon Bayansa Su Halarci Hawan Sallah

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.