ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS Da Kuma Gana Da Takwarorinsa Na Habasha Da Afirka Ta Kudu

by CGTN Hausa
2 years ago
Kasar sin

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya halarci taron ministocin kungiyar BRICS a jiya Litinin a birnin Nizhni Novgorod na kasar Rasha.

Yayin taron, Wang Yi ya ce, hadin gwiwar kasashen BRICS ya gudana cikin sauri da inganci a cikin shekara daya da ta gabata, inda har BRICS ta shigar da sabbin mambobi, matakin da ya bude sabon babin hadin gwiwar kasashe masu tasowa dake dogaro da karfinsu, abin da ya sa BRICS ke kara jan hankalin duniya.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Inganta Tsarin Kamfanoni Na Zamani Mai Halayyar Musamman Ta Sin
  • Kasar Sin Ta Gada Tare Da Raya Al’Adun Da Suka Shafi Bikin Gargajiya Na Duanwu

Wang Yi ya ce, “dole ne mu nace ga tabbatar da adalci da gaskiya, mu bi hanyar da ta dace da yanke shawara yadda ya kamata, duba da cewa ana fuskantar ja-in-ja tsakanin ra’ayin mu’amalar bangarori daban daban a duniya da na babakere, da ma ra’ayin bangarori da na kashin kai.”

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa ya kamata a yi amfani da tsare-tsare da tasirin siyasar kungiyar yadda ya kamata don mai da BRICS wani sabon tsari mai yakini na hadin kan kasa da kasa da bude kofa dake dogaro da tushen kasuwanni masu saurin ci gaba da karfin kasashe masu tasowa.

Mahalarta taron sun yabawa babban tasiri da ci gaban shigar da sabbin mambobi da BRICS ya samu, inda suke ganin cewa, shigar da karin mambobi cikin kungiyar za ta gaggauta samar da iko tsakanin bangarori da dama a duniya da ingiza doka da odar kasa da kasa mai adalci da daidaito, kuma sun amince da tsarin shigar da kasashen hulda cikin kungiyar, inda kuma aka gabatar da “Hadaddiyar Sanarwa Game Da Ganawar Ministocin Wajen Kasashen BRICS”.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sannan a yayin taron, Wang Yi ya gana da takwaransa na Habasha, Taye Atske Selassie, a birnin Nizhny Novgorod na kasar Rasha.

Da yake bayyana Habasha a matsayin muhimmiyar kasa a nahiyar Afrika, kuma mai masaukin hedkwatar kungiyar Tarayyar Afrika (AU), Wang Yi ya ce, zaman lafiya da kwanciyar hankalin kasar na da muhimmanci ga nahiyar. Ya kara da cewa, a shirye Sin take ta zurfafa abota cikin kowanne yanayi, da fadada hadin gwiwa a bangarori daban daban, da kuma ingiza samun karin nasarori a dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, domin jama’arsu su amfana da su.

A nasa bangare, Taye Atske Selassie ya ce, gwamnati da al’ummar Habasha na maraba da daukaka dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa ta abota bisa manyan tsare-tsare a kowanne yanayi. Ya kara da cewa, kasar Sin ce babbar mai zuba jari a Habasha, haka kuma inda ta fi shigar da kayayyakinta, kana dangantakar dake tsakaninsu ta bunkasa tattalin arziki da kyautata zamantakewar Habasha.

Bugu da kari, Wang Yi ya gana da takwaransa ta Afirka ta kudu Naledi Pandor, a garin Nizhni Novgorod na kasar Rasha.

Yayin zantawar tasu a jiya Talata, Wang Yi ya taya Afirka ta kudu murnar gudanar da babban zaben kasa cikin nasara. Yana mai bayyana yadda Sin ke dora muhimmancin gaske ga ci gaban Afirka ta kudu, a matsayin ta na babbar kasa mai tasowa. Ya ce Sin a shirye take ta yi aiki tukuru tare da sassan kasa da kasa a fannin tsare tsare, da samar da murya mai ma’ana, kuma mai daidaito, game da muhimman batutuwa dake addabar duniya, kamar rikicin Ukraine, kana tana fatan ba da gudummawa ga wanzar da zaman lafiya da daidaito a duniya.

A nata bangare kuwa, Naledi Pandor, cewa ta yi Afirka ta kudu na jinjinawa kokarin kasar Sin, na ganin an warware rikicin Ukraine ta hanyar siyasa, da yayata bukatar dakatar da bude wuta a Gaza. Ta ce Afirka ta kudu a shirye take ta karfafa hadin gwiwa da Sin, karkashin dandalolin kasa da kasa, irin su kungiyar BRICS, da G20, don tabbatar da an cimma nasarar raya ci gaban tsare tsaren da ake gudanarwa karkashin su yadda ya kamata. (Masu Fassarawa: Saminu Alhassam, Fa’iza Mustapha, Amina Xu)

Kasar sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Sarkin Kano Na 15 Ya Umarci Hakiman Da Ke Goyon Bayansa Su Halarci Hawan Sallah

Sarkin Kano Na 15 Ya Umarci Hakiman Da Ke Goyon Bayansa Su Halarci Hawan Sallah

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.