• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mafi Karancin Albashi: Gwamnati Ta Buƙaci Ma’aikata Su Karɓi Abin Da Ba Zai Gurgunta Tattalin Arziki Ba

by Sulaiman
12 months ago
in Labarai
0
Mafi Karancin Albashi: Gwamnati Ta Buƙaci Ma’aikata Su Karɓi Abin Da Ba Zai Gurgunta Tattalin Arziki Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) da ta amince da mafi ƙarancin albashi na ƙasa wanda ba zai gurgunta tattalin arzikin ƙasa ba, kuma ya kai ga korar ma’aikata da dama.

Idris ya yi wannan roƙo ne a lokacin da yake buɗe taron ƙungiyar limaman Kirista ta Charismatic Bishops of Nijeriya na 2024 a Abuja ranar Laraba.

  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 8, Sun Ceto Mutane 87 A Katsina
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji A Kan Hanyar Abuja Zuwa Nasarawa

A cikin wata sanarwa da Mataimaki na Musamman ga Ministan kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabi’u Ibrahim ya fitar, an ruwaito cewa Idris ya jaddada buƙatar samar da ingantaccen tsarin albashi mai ɗorewa wanda zai daidaita buƙatun ma’aikata da yanayin tattalin arzikin ƙasa.

Ya bayyana ƙudirin gwamnati na sake duba mafi ƙanƙantar albashi amma ya yi gargaɗi kan buƙatu da ka iya cutar da tattalin arzikin ƙasar nan.

Ministan ya bayyana ƙoƙarin da gwamnati ke yi na rage tsadar rayuwa da kuma ƙara wa ‘yan Nijeriya ƙarfin yin sayayya ta hanyar shirye-shirye kamar shirin Shugaban Ƙasa na samar da motoci masu aiki da gas (CNG), wanda ke da nufin rage kuɗin sufuri da kashi 50 cikin ɗari.

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Ya ce: “Kamar yadda na sha faɗa, Gwamnatin Tarayya ba ta adawa da ƙarin albashi ga ma’aikatan Nijeriya amma muna ci gaba da bayar da shawarwarin samar da ingantaccen tsarin albashi ga ma’aikata – tsarin albashin da ba zai gurgunta tattalin arzikin ƙasa ba har ya kai ga korar ma’aikata da yawa tare da kawo cikas ga jin daɗin ‘yan Nijeriya kusan miliyan 200.

“Muna so ‘yan Ƙungiyar Ƙwadago su fahimci cewa sauƙin da ‘yan Nijeriya ke jira, kuma suka cancanta a ba su, ba zai zo ne kawai ta hanyar ƙarin albashi ba.

“Zai zo ne kuma a ƙoƙarin rage tsadar rayuwa da kuma tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya sun samu ƙarin kuɗaɗe. Kuma a nan ne shirye-shirye kamar shirin CNG na Shugaban Ƙasa ke shigowa.

“Ta hanyar maye gurbin amfani da man fetur da iskar gas, wannan shirin kaɗai zai rage kuɗin sufuri da kashi 50 cikin ɗari.”

Ministan ya yi kira ga malaman addinin Kirista da su goyi bayan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu wajen ganin an farfaɗo da Nijeriya tare da yin addu’ar hikima da jagora a daidai lokacin da ƙasar nan ke fuskantar ƙalubalen da ke addabar ta.

“Haƙiƙa, Coci, a tsawon tarihin ƙasar mu, ta kasance abokiyar hulɗa ga gwamnati wajen fafutikar tabbatar da zamantakewa da samar da muhimman ayyukan jin daɗin jama’a kamar asibitoci da makarantu, da kuma cusa ɗabi’u na gari a cikin ‘yan ƙasar mu.

“Ko da muna cikin mawuyacin hali na wucin-gadi amma wanda ya zama dole, ba hutu Shugaban Ƙasa ke yi ba. Ya ƙudiri aniyar tabbatar da cewa an fitar da matakan agaji da dama domin amfanin kowane ɓangare na al’ummar Nijeriya.

“Yanzu, a nan ne ku a matsayin ku na malaman addinin Kirista, a matsayin ku na shugabannin addini da ake mutuntawa da kuma masu faɗa a ji, za ku shigo. A matsayin mu na gwamnati, muna buƙatar goyon bayan ku, shawarwarin ku, da ra’ayoyin ku.

“Abu mafi muhimmanci kuma shi ne muna buƙatar ku san ƙoƙarin da ake yi, da ƙalubalen da ake fuskanta, domin ku taimaka mana mu sanar da waɗannan ikilisiyoyin ku da sauran jama’a.”

Yayin da ya bayyana cewa Shugaba Tinubu ya hau karagar mulki ne a lokacin da aka fi fuskantar ƙalubale a Nijeriya, Idris ya ce Shugaban Ƙasar na bakin ƙoƙarin sa wajen ganin an samu cigaba mai ɗorewa a faɗin ƙasar nan.

Ya ce: “Babu wanda ke shakkar cewa Shugaban Ƙasa ya tashi tsaye ne tare da jajircewa da aikata abin da ya dace. A cikin shekarar da ta gabata ya aiwatar da muhimman gyare-gyare masu muhimmanci da nufin mayar da ƙasar mu kan turbar haɓaka, wadata, da samun cigaba mai ɗorewa.

“Shugaba Tinubu bai taɓa ƙin amincewa da gaskiyar wannan raɗaɗin da ake ji ba. A cikin jawabin sa na Ranar Dimokiraɗiyya da ya gabatar wa al’ummar ƙasar da safiyar yau, Shugaba Tinubu ya taƙaita shi da kyau da ya ce: ‘Mun ɓullo da gyare-gyare ne domin samar da tushe mai inganci don samun cigaba a nan gaba.

“Babu shakka sauye-sauyen sun haifar da wahalhalu. Amma duk da haka, su ne gyare-gyaren da ake buƙata domin gyara tattalin arziki cikin dogon lokaci ta yadda kowa zai samu damar tattalin arzikin, da samun albashi mai kyau, da kuma ladar ƙoƙarin sa da ayyukan sa.'”

Idris ya ƙara da cewa: “Haƙiƙa, a matsayin mu na al’umma, muna jure wa sadaukarwa na ƙanƙanen lokaci domin samun fa’ida ta dogon lokaci. Mun samu ƙwarin gwiwa da Nijeriyar da ba za a bar kowa a baya ba.”

Ya yi nuni da cewa ma’aikatar sa za ta haɗa kai da malaman Kirista wajen aiwatar da shirin wayar da kan jama’a na ƙasa, wato ‘National Values Charter’.

“Saboda haka, bari in ce Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai za ta yi matuƙar farin ciki da haɗa kai da babban Taron Charismatic Bishops yayin da muke aiwatar da shirin mu na wayar da kan jama’a, wato ‘National Values Charter’, wanda ke neman cusa ɗabi’u masu ɗorewa a cikin zukata da tunanin ‘yan ƙasar mu”, inji shi.

Ya jaddada cewa Shugaba Tinubu ya aiwatar da manufofin sa na Sabunta Fata yayin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da samun ƙarin nasarori a sassa daban-daban na tattalin arzikin mu.

“Shugaban Ƙasa ya yi aiki tuƙuru don daidaita tattalin arzikin ƙasar ta hanyar janye tallafin man fetur maras ɗorewa da kuma haɗewar kasuwar canjin kuɗaɗe, a matsayin muhimman matakai na karkatar da kuɗaɗe zuwa sassa masu mahimmanci kamar kiwon lafiya, ilimi, da ababen more rayuwa.”

Tun da farko, sai da Shugaban ƙungiyar ‘Charismatic Bishops Conference’ na Ƙasa, Archbishop Leonard Bature Kawas, ya yi alƙawarin biyayya da goyon baya ga gwamnatin Shugaba Tinubu, tare da jaddada cewa za su ci gaba da haɗa kai da gwamnati domin cimma burin ta ga Nijeriya.

Ya ƙara da cewa sun gayyaci ministan wanda Musulmi ne domin ya buɗe taron nasu saboda suna ga cewa ɗan Nijeriya ne mara ƙabilanci wanda ba ya nuna bambancin addini.

Archbishop Kawas ya ce limaman coci daga jihohi 36 na tarayya da ƙasashe 21 ne suka halarci taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kungiyar GwamnoniNlcTUC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojojin Nijeriya Sun Kashe Ƴan Bindigar Daji A Dajin Taraba, Sun Ƙwato Makamai Da Kayan Aiki

Next Post

Hukuma A Kano Ta Damƙe Mutane 2 Kan Zargin Zamba

Related

Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

10 minutes ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

1 hour ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

2 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

5 hours ago
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
Labarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

5 hours ago
Next Post
Hukuma A Kano Ta Damƙe Mutane 2 Kan Zargin Zamba

Hukuma A Kano Ta Damƙe Mutane 2 Kan Zargin Zamba

LABARAI MASU NASABA

Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.